Gwamnati Ta Saki Sunayen Likitoci 2 da Take Nema Ruwa a Jallo, Sun Aikata Laifi

Gwamnati Ta Saki Sunayen Likitoci 2 da Take Nema Ruwa a Jallo, Sun Aikata Laifi

  • Gwamnatin Akwa Ibom ta saki sunayen wasu likitoci biyu da take nema ruwa a jallo bayan sun bar aiki ba tare da izini ba
  • Kwamishinan lafiya na jihar, Ekem John, ya ce gwamnati ta kashe kudade masu yawa wajen horar da likitocin biyu
  • Ya ce ko dai su dawo bakin aikinsu, ko su biya kudin da gwamnati ta kashe a karatunsu, ko kuma su gamu da fushin doka

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Akwa Ibom - Gwamnatin Akwa Ibom ta ayyana wasu likitoci biyu a matsayin wadanda take nema ruwa a jallo bayan da suka gudu daga bakin aikinsu a ma'aikatar lafiya ta jihar.

A ranar Litinin, kwamishinan lafiya na jihar, Ekem John, ya bayyana wa manema labarai cewa gwamnatin Akwa Ibom ce ta dauki nauyin karatun likitocin biyu har na tsawon shekaru takwas.

Kara karanta wannan

Wutar lantarki ta samu matsala, mutane za su shiga duhu a jihohi 4 a Najeriya

Gwamnatin Akwa Ibom na neman wasu likitoci 2 ruwa a jallo.
Wasu likitoci na gudanar da gwaje-gwaje a cikin asibiti. Hoto: Getty Images A kula: Mutanen da ke cikin hoton ba su da alaka da labarin.
Source: Getty Images

Gwamnatin Akwa Ibom na neman likitoci ruwa a jallo

Premium Times ta ruwaito cewa, Ekem John ya ce daga cikin likitocin da ake nema akwai, Uduakabasi Ita, kwararren likita a fannin binciken cututtuka da hoton X-ray.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai kuma Mfonobong George Bassey, kwararren likita a fannin binciken cututtukan jini, wanda shi ma ake nema ruwa a jallo.

Ya ce likitocin suna da zaɓi na ko dai su dawo bakin aiki, ko kuma su maida kudin da gwamnatin ta kashe wajen daukar nauyin karatunsu.

Gwamnati ta gargadi likitocin 2 da ake nema

Ekem John ya shaidawa 'yan jarida a babban birnin Uyo cewa:

"Za mu bi diddiginsu har sai mun kama su. Babu wata kasa da za su ce da ba za mu iya tuntubar kungiyar likitoci ba, za mu tabbatar sun rasa lasisin aiki.
"Yana da matukar amfani a gare su, su gaggauta miƙa kansu ga ma'aikatar lafiya ta jihar Akwa Ibom, tun kafin fushin doka ya sauka a kansu."

Kara karanta wannan

Wata sabuwa: Gwamna ya ayyana dokar ta baci a jiharsa, zai dauka ma'aikata 2,000

Kwamishinan ya fada wa likitocin su kuka da kansu, kan abin da zai iya biyo baya, domin tuni ta mika lamarin ga majalisar likitocin Najeriya ta MDCN, wacce za ta iya janye lasisin aikin su.

Ya ƙara da cewa, nan gaba, duk wani ma'aikacin lafiya da gwamnatin jihar ta daukin nauyin karatunsa zai yi aiki a jihar har tsawon shekarun da aka amince da su kafin a ba shi izinin yin murabus.

Gwamnatin Akwa Ibom ta nemi likitocin su mika kansu ga ma'aikatar lafiya ta jihar.
Taswirar jihar Akwa Ibom da ke a Kudancin Najeriya. Hoto: Legit.ng
Source: Original

Ƙarancin likitoci a Najeriya

Najeriya na fuskantar matsanancin ƙarancin likitoci da sauran ma’aikatan lafiya, saboda yawancinsu suna son yin aiki a ƙasashen waje don samun albashi mai kyau da ingantaccen yanayin rayuwa.

A jihohi da dama a Najeriya, ƴan likitocin da ake da su a asibitocin gwamnati, su ne dai za a samu suna da nasu asibitocin masu zaman kansu.

A kwanan baya ne dai aka samu matsala a Akwa Ibom, inda wata mata da jaririnta suka mutu bayan an yi mata tiyatar haihuwa a wani asibitin gwamnati a jihar. Iyayen wadda abin ya shafa sun zargi ma'aikatan asibitin da rashin kula.

Likitoci sun shiga yajin aiki a Najeriya

Kara karanta wannan

A karshe, Likitoci sun shiga yajin aiki, sun rufe asibitocin gwamnati baki daya

A wani labarin, mun ruwaito cewa, kungiyar likitoci ta ARD reshen Abuja, ta sanar da shiga yajin aikin sai baba ta gani daga ranar 15 ga Satumba, 2025.

Likitocin sun bayyana cewa, gwamnati ta ki biyan hakkokinsu, ta gaza daukar sababbin likitoci, lamarin da ya jefa asibitoci cikin mawuyacin hali.

Kungiyar ta ce asibitoci 14 na babban birnin kasar na fama da karancin ma’aikata, lamarin da ke tilasta likitoci yin aikin da ya wuce kima, har ya shafi lafiyarsu.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com