Matasa Za Su Wartsake, Gwamna Ya Kafa Tarihi bayan Naɗa Hadimai 1,200 a Jiharsa

Matasa Za Su Wartsake, Gwamna Ya Kafa Tarihi bayan Naɗa Hadimai 1,200 a Jiharsa

  • Gwamnatin Ogun ta kafa tarihi a jihar bayan nada hadiman gwamna na musamman mafi yawa a kan harkokin siyasa
  • An nada mataimakan na musamman kan siyasa 1,200 domin inganta alaka da jama’a cikin mulki saboda kara kusanci da gwamnati
  • Majiyoyi sun ce an yi haka domin yada ayyuka da amfanin dimokuraɗiyya a dukkan kananan hukumomin da ke jihar

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abeokuta, Ogun - Gwamnatin jihar Ogun ta nada mataimaka na musamman kan harkokin siyasa fiye da 1,000 a jihar.

Gwamna Dapo Abiodun ya amince da nadin hadiman 1,200 domin su zama wakilai, su kuma ƙarfafa shiga jama’a cikin harkokin mulki a fadin jihar.

Gwamna Abiodun ya nada hadimai 1,200 a Ogun
Gwamnan jihar Ondo a Kudancin Najeriya, Dapo Abiodun. Hoto: Prince Dapo Abiodun.
Source: Facebook

Mai ba da shawara na musamman kan yada labarai da dabaru ga Gwamna Dapo Abiodun, Kayode Akinmade, shi ya tabbatar da haka a shafin Facebook.

Kara karanta wannan

Matukan jirgin sama sun sha giya da kwaya, sun kusa halaka mutane a Najeriya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Musabbabin nada hadimai 1,200 a jihar Ogun

Akinmade ya bayyana wannan matakin nada hadiman a matsayin dabarar inganta dimokuraɗiyya da cudanya da al'umma tun daga tushe.

Ya ce:

"Domin cika alkawarin ta na zurfafa shiga harkokin dimokuraɗiyya da kuma faɗaɗa damar samun ribar dimokuraɗiyya.
"Gwamnatin Ogun ta naɗa mataimaka a bangaren siyasa 1,200 domin su zama jakadun kawo sauyi tare da ƙarfafa haɗin kan jama’a a fadin jihar."

Yadda aka fasalta nadin hadimai 1,200 a Ogun

A cewar Akinmade, mataimakan biyar daga kowace mazaba cikin mazabu 236 na Ogun za su tabbatar da shiga jama’a sosai, tare da haɗa gwamnati da talakawa.

Ya kara da cewa:

“Sababbin mataimakan kan harkokin siyasa za su tallafa wajen isar da amfanin dimokuraɗiyya, bayyana bukatun mazabunsu, tare da isar da bukatun ga gwamnatin jiha.
"Har ila yau, ana tsammanin masu mukaman za su mayar da martanin da gwamnatin ta yi game da bukatun yadda ya dace ga al'umma da suka tura korafinsu.

Kara karanta wannan

Ana kukan farashin taki, Shettima ya ce a raba wa manoma Naira biliyan 250

Gwamna ya bukaci sababbin hadimai su ba da gudunmawa a Ogun
Gwamna Dapo Abiodun na jihar Ogun. Hoto: Price Dapo Abiodun.
Source: Facebook

Rokon Gwamna ga sababbin hadimai da ya nada

Akinmade ya ƙara da cewa suna kuma da alhakin bayar da sahihan rahotanni daga gwamnati zuwa mazabu da kuma daga jama’a zuwa gwamnati kai tsaye.

Mista Akinmade ya jaddada cewa wannan shiri da daga cika alkawuran zaben Gwamna Dapo Abiodun na tafiyar da gwamnati mai mu'amala da kowa da kowa.

Gwamnatin ta kuma bukaci sababbin mataimakan su bayar da gudummawa wajen ci gaban mazabu, kananan hukumomi da kuma jihar gaba ɗaya.

Gwamna Abiodun ya maka Sarki a kotu

A baya, mun ba ku labarin cewa gwamnatin jihar Ogun ta gurfanar da sarkin Obafemi, Oba Taofeek Owolabi a kotu bisa zargin kwace da sayar da fili ba bisa ka’ida ba.

An ce Sarkin ya sayar wa wani mutumi wata gona a kan ₦75m, amma ya ki ba masu gonar kuɗinsu, sai ma ya tura masu 'yan daba suka yi musu cin mutunci.

Kara karanta wannan

Tawagar kasar Rasha ta dura Najeriya, ta sauka a jihar Neja

Duk da gayyatar majalisar dokokin jihar da majalisar sarakunan gargajiya, Oba ya ƙi mika wuya, lamarin da ya kai ga gurfanar da shi.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.