An Gano Jami’an Tsaro na Taimakawa Yan Bindiga a Bidiyo? Gaskiya Ta Bayyana

An Gano Jami’an Tsaro na Taimakawa Yan Bindiga a Bidiyo? Gaskiya Ta Bayyana

  • An yi ta yada wani faifan bidiyon jami'an tsaro da ake zargin suna taimakawa yan bindiga a cikin wani daji da aka yi zargin a Najeriya ne
  • Wannan ba shi ne karon farko ba da ake yada irin wannan bidiyo wanda ke kara raunana guiwar jami'an sojoji da ke bakin kokarinsu ba
  • Binciken kwa-kwaf ya karyata bidiyon da ake yadawa, inda ake ikirarin sojojin Najeriya na ba ’yan bindiga masu yin ta'adi goyon baya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - A Najeriya an sha samun wasu rahotanni da ke yada cewa jami'an tsaro na goyon bayan yan bindiga a cikin wani daji.

Wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta yana cewa sojojin Najeriya na marawa ’yan bindiga baya da aka gano a cikin daji.

Kara karanta wannan

An dura kan Bashir Ahmad game da sukar kiran zanga zanga a Najeriya kamar Nepal

An yi binciken kan yada bidiyon sojoji na taimakon yan bindiga
Gungun yan bindiga a daji da dakarun sojojin Najeriya. Hoto: HQ Nigerian Army.
Source: Twitter

Binciken kwa-kwaf na Zagazola Makama ya tabbatar da cewa wannan batu ƙarya ne kuma an yi domin rudar da jama'a ne.

Yadda ake yada bidiyon karya kan jami'an tsaro

Wannan ba shi ne karon farko ba da ake samun irin wannan matsala wanda ake yada bidiyo da ke tayar da hankula da saka shakku a yaki da ta'addanci.

Irin wannan bidiyo da ake yadawa na kara jawo tasgaro kan yaki da ta'addanci da ake ta kokarin yi a Najeriya musamman ga jami'an tsaro.

Rundunar 'yan sanda ta musanta rade-radin cewa jirgin sama ya kai kayan abinci ko makamai ga 'yan bindiga a jihar Kogi.

Karin haske daga rundunar 'yan sanda kan lamarin

'Yan sanda sun bayyana cewa jirgin ya shiga aikin yaki da 'yan bindiga ne tare da hadin gwiwar jami’an tsaro da 'yan banga a Obajana.

Rundunar ta bukaci jama’a da su daina yarda da labaran karya, su rika sauraron bayanai daga hukumomin tsaro tukuna a koyaushe domin gujewa fadawa irin wannan tarko.

Kara karanta wannan

An nada Farfesa Maqari limami a masallacin ka'abah? malamin ya yi karin haske

An karyata bidiyon da ake yadawa wai sojoji na taimakon yan bindiga a daji
Hafsan rundunar tsaro a Najeriya, Janar Christopher Musa. Hoto: Defence Headquarters Nigeria.
Source: Facebook

Bincike ya karyata bidiyon sojoji da 'yan bindiga

Majiyoyi sun gano bidiyon da ake yadawa ya fara bayyana a farkon 2024 daga rikicin Darfur a Sudan kuma ba shi da alaƙa da Najeriya.

Masana sun ce irin waɗannan hotuna na karya suna karya kwarin gwiwar dakarun yaki da ta’addanci, suna kuma ƙara yaɗa tashin hankali a al’umma.

An ja hankalin jama’a su daina yada bidiyoyi marasa tushe saboda hakan na taimakawa ’yan ta’adda da bata kokarin jami’an tsaro.

Binciken ya ce ya kamata a jajirce wajen karyata labaran ƙarya tare da tabbatar da jama’a na samun sahihan bayanai masu inganci.

'Yan bindiga, sojoji sun gwabza fada a Katsina

Kun ji cewa dakarun Operation Fansan Yanma tare da taimakon sauran jami'an tsaro sun fatattaki ‘yan bindiga a karamar hukumar Malumfashi da ke jihar Katsina.

A yayin da ake musayar wuta, 'yan ta'addan sun kashe shugaban mafarauta, Usman Lawal, sannan su ma an kashe masu mutum daya.

Kara karanta wannan

'Duk da fara shirin sulhu, 'Yan bindiga sun yi kisa, an sace mutane masu yawa a Katsina

Harin na yammacin Talata, 9 ga Satumba, 2025, na zuwa ne bayan Gwamna Dikko Radda ya yi magana kan sulhu da 'yan bindiga a Katsina.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.