'Yan Sanda Sun Gayyaci El Rufai da Wasu Ƴan Siyasa 6 kan abin da Ya Faru a Kaduna

'Yan Sanda Sun Gayyaci El Rufai da Wasu Ƴan Siyasa 6 kan abin da Ya Faru a Kaduna

  • Rundunar ’yan sanda ta gayyaci tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar ADC a jihar
  • An gayyace su ne kan zargin hada baki, tada zaune-tsaye, ɓarnatar da dukiya da kuma jikkata mutane a wani taron siyasa
  • Nasir El-Rufai ya yi martani ga 'yan sanda kan abin da ya faru a Kaduna yayin da jigon ADC ya magantu kan takardar gayyatar

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kaduna - Rundunar ‘yan sandan Kaduna, ta gayyaci tsohon gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufai da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar ADC domin amsa tambayoyi.

A cewar wata wasika da Legit Hausa ta gani, an gayyaci El-Rufai ne bisa zargin hada baki, da tayar da tarzoma, da kuma raunata mutane.

'Yan sanda sun gayyacin El-Rufai da wasu kusoshin ADC domin amsa tambayoyi
Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai lokacin yana gwamna, da shugaban 'yan sanda, Kayode Egbetokun. Hoto: @elrufai, @PoliceNG
Source: Facebook

Kaduna: 'Yan sanda sun gayyaci El-Rufai

Mataimakin kwamishinan 'yan sanda, mai kula da sashen binciken manyan laifuffuka (CID), Uzainu Abdullahi ne ya sanya wa takardar hannu, a ranar 4 ga Satumba, 2025, inji rahoton Channels TV.

Kara karanta wannan

El Rufai ya fusata bayan 'yan sanda sun hana taron ADC a Kaduna

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sunayen wadanda ake gayyata, da aka ambata a cikin takardar sun hada da:

  1. Malam Nasir El-Rufai
  2. Bashir Sa’idu
  3. Jafaru Sani
  4. Ubaidullah Mohammed (30)
  5. Nasiru Maikano
  6. Aminu Abita
  7. Ahmed Rufa’i Hussaini (Mikiya)

Sanarwar da aka aike wa shugaban jam'iyyar ADC na Kaduna, ta ce:

"An buƙace ka, ka kawo wadanda aka ambata zuwa sashin SCID domin amsa tambayoyi kan zarge-zargen da masu ƙarar suka kawo a kansu a ranar 8 ga Satumba, 2025."

Martanin jam’iyyar ADC a Kaduna

Jafaru Sani, mataimakin shugaban ADC na Arewa maso Yamma, wanda sunansa ya fito cikin jerin wadanda ake gayyata, ya ce mafi yawansu sun samu labarin gayyatar ne ta shafukan sada zumunta.

A zantawarsa da jaridar Daily Trust, Jafaru Sani, ya ce ba zai iya yin karin bayani game da gayyatar ba tukunna.

Sabani tsakanin gwamnati da El-Rufai

A makon da ya gabata, gwamnatin Kaduna da El-Rufai sun yi musayar maganganu kan tashin hankali da ya faru a wani taron ADC da aka shirya a jihar.

Kara karanta wannan

Biyan 'yan bindiga kudi: Baba-Ahmed ya yi wa El Rufai raddi mai zafi

Gwamnatin Kaduna ta zargi tsohon gwamnan da kokarin tayar da rikici da jawo rarrabuwar kawuna a jihar, zargin da ya El-Rufai ya musanta.

Mun ruwaito cewa, Dr. Suleiman Shuaibu, kwamishinan tsaro na jihar, ya ce gwamnati ba za ta zuba ido ta kyale tsohon gwamnan da ya bar jihar a ruɗani ya jefa ta cikin wani sabon rikici ba.

Mallam Nasir El-Rufai ya ce matakan da 'yan sanda suka dauka bayan abin da ya faru a Kaduna ya saba wa dokar kasa.
Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai yana jawabi a wani taro. Hoto: @elrufai
Source: Twitter

Nasir El-Rufai ya kare kansa

A martanin da ya yi, El-Rufai ya ce gwamnatin Uba Sani na kokarin kulle bakin 'yan adawa ta hanyar zarge-zargen da ba su da tushe.

Ya ce jam’iyya mai mulki na amfani da rikicin da ya faru a taron ADC a matsayin hujjar hana adawa yin tasiri a jihar.

El-Rufai ya soki 'yan sandan Kaduna

A wani labarin, mun ruwaito cewa, Nasir El-Rufai ya bayyana matuƙar rashin jin daɗinsa kan umarnin ‘yan sanda na hana taron shugabannin ADC a Kaduna.

Tsohon gwamnan jihar na Kaduna ya ce abin da 'yan sandan suka yi ya saba da tanade-tanaden kundin tsarin mulki na Najeriya.

El-Rufai ya zargi kwamishinan ‘yan sandan Kaduna da karbo umarnin kotu da ya hana taron ba tare da an bin hanyoyin da suka dace ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com