Gwamnonin Arewa Sun Gana da Tinubu a Abuja, Sun Roƙi Manyan Alfarma 2

Gwamnonin Arewa Sun Gana da Tinubu a Abuja, Sun Roƙi Manyan Alfarma 2

  • Gwamnonin Arewa maso gabashin Najeriya sun yi wata ganawa da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a Abuja
  • Gwamnonin yankin sun tura bukatu na musamman ga shugaban Najeriyan domin kawo sauyi da ci gaba a jihohinsu
  • Babagana Zulum shi ya jagoranci gwamnonin Arewa maso Gabas wajen ganawar inda suka bukaci kammala manyan ayyukan hanyoyi 17

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya jagoranci tawagar gwamnonin Arewa domin ganawa da Bola Tinubu.

Zulum ya jagoranci gwamnonin ne daga Arewa maso Gabas domin tura bukatunsu ga shugaban a yau Laraba a Abuja.

Gwamnonin Arewa sun gana da Tinubu a Abuja
Zulum ya jagoranci gwamnonin Arewa maso Gabas domin ganawa da Tinubu. Hoto: Isma'ila Uba Misilli, Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Facebook

Bukatun gwamnonin Arewa maso gabas ga Tinubu

Daraktan yada labaran gwamna Inuwa Yahaya na Gombe, Isma'ila Uba Misilli ya tabbatar da haka a shafin Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An gudanar da taron ne a fadar shugaban kasa da ke Abuja, inda aka tattauna batutuwan masu muhimmanci.

Kara karanta wannan

Kura kuren da ke fitowa daga Aso Rock sun sa an taso Tinubu da hadimansa a gaba

Daga cikin batutuwan akwai kammala hanyoyi 17 masu muhimmanci a yankin domin kawo ci gaba.

Haka kuma, an bukaci a ci gaba da aikin hako mai a rijiyoyin Kolmani da na Tafkin Chadi domin bunkasa tattalin arzikin yankin.

Gwamnonin da suka yi zama da Tinubu

Gwamnonin da suka halarta sun hada da Muhammadu Inuwa Yahaya na Gombe, Bala Muhammad na Bauchi, Mai Mala Buni na Yobe.

Sauran sun hada da Agbu Keffas na Taraba da Ahmadu Umaru Fintiri daga jihar Adamawa wadanda gaba daya suka mara wa Zulum baya a matsayin shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa maso Gabas.

Gwamna Zulum ya tura bukatun gwamnonin Arewa ga Tinubu
Gwamnonin Arewa maso Gabas yayin taronsu a Jalingo sun roki Tinubu. Hoto: Agbu Kefas.
Source: Facebook

Hanyoyin da ake neman Tinubu ya gyara

A jawabinsa, Zulum ya roki shugaban kasa ya kammala manyan ayyukan hanyoyi da gina sababbin hanyoyin da ke hade jihohin yankin gaba daya.

Hanyoyin sun hada da Kano-Maiduguri, Port Harcourt-Jos-Bauchi-Maiduguri, Bama-Mubi-Yola, Wukari-Jalingo-Yola, Duguri-Mansur da kuma Bauchi-Gombe-Biu-Damaturu.

Sauran sun hada da Damaturu-Geidam, Bauchi-Ningi-Nasaru-Babaldo, Gombe-Potiskum, Damaturu-Biu, Alkaleri-Futuk, Maiduguri-Damboa-Yola da kuma Gombe-Dukku-Darazo.

Bugu da kari akwai Biu-Gombe, Ibi-Shamdam, Maiduguri-Monguno-Baga da kuma Maiduguri-Ngala-Bama-Banki, wadanda ake ganin suna da matukar muhimmanci.

Kara karanta wannan

Garambawul a jihohi: Gwamnonin Najeriya 6 Sun Rushe Majalisun Zartarwa a 2025

Alkawuran gwamnonin ga Bola Tinubu

Zulum ya gode wa shugaban kasa kan jajircewar dawo da zaman lafiya a yankin inda ya jaddada masa goyon bayansu.

Zulum ya ce:

“Mai girma shugaban kasa, gwamnonin Arewa maso Gabas muna ba ka daraja ta musamman kuma dukanmu mun yanke shawarar kasancewa tare da kai."

Shugaba Tinubu a martaninsa ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da daukar matakan da suka dace domin bunkasa yankin Arewa maso Gabas.

Gwamnonin Arewa sun yi kira ga Tinubu

A baya, mun ba ku labarin cewa gwamnonin yankin Arewa maso Gabas sun fito sun yi gargadi na musamman game da abin da zai faru a Najeriya a 2026.

Gwamnonin sun bayyana cewa za a samu tsadar kayan noma da zai iya haddasa ƙarancin abinci a shekarar 2026 da ke tafe.

Sun roƙi gwamnati ta kara tallafin manoma da kuma fadada shirin noma na damina da rani domin kauce wa matsalolin abinci.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.