Faransa Ta Dawo da Ƙoƙon Kawunan Sarakuna a Afrika bayan Kashe Su

Faransa Ta Dawo da Ƙoƙon Kawunan Sarakuna a Afrika bayan Kashe Su

  • Faransa ta cika alkawarin da ta dauka ga Madagascar bayan shafe shekaru da dama game da kisan wasu sarakuna
  • Ƙasar ta cika alkawarin ne bayan dawo da kokon kawunan sarakuna uku bayan shekaru 128 da aka kashe su
  • Faransa ta mika su bisa sabuwar dokar 2023 wacce ta sauƙaƙa dawo da kayan tarihi a taron ban girma a Antananarivo

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Antananarivo, Madagascar - Jami'an gwamnatin kasar Madagascar sun gana da wasu wakilan kasar Faransa a wani gagarumin taro.

A ranar Talata, Madagascar ta gudanar da wani babban biki na dawo da kokon kawunan sarakuna uku da aka kwashe shekaru 128 da suka gabata.

An dawo da kokon kawunan sarakuna daga Faransa
Jami'an tsaro yayin da suka karbi kokon kawunan sarakunan Madagascar daga Faransa. Hoto: Le Monde.
Source: Getty Images

Madagascar ta karbi kokon kawuna sarakuna daga Faransa

Ana kyautata zaton daya daga cikinsu kawun Sarki Toera ne na kabilar Sakalava, wanda aka kashe lokacin mamayar mulkin mallaka, cewar Al Jazeera.

Kara karanta wannan

Dattawan Arewa sun cimma matsaya kan rashin tsaro, sun sanar da Shugaba Tinubu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rahotanni sun bayyana cewa, kawunan da suka hada da na Sarki da jarumansa biyu, sojojin Faransa ne suka kwace su a 1897, suka tafi da su Paris.

A can aka ajiye su a gidan kayan tarihi a matsayin kayan ganima na yaki, kamar yadda miliyoyi suka tabbatar.

An mika kokon kawunan ga hukumomi wanda kasar Faransa ta yi bisa sabuwar dokar 2023 wacce ta ba da damar dawo da gawarwaki da aka kwace a lokacin mulkin mallaka.

Sun iso Antananarivo ranar Litinin da dare, inda wakilan Sakalava cikin kayan gargajiya suka tarbe su a filin jirgi da girmamawa, France 24 ta ruwaito.

Madagascar ta karbi kokon kawunan sarakuna daga Faransa
Shugaban kasa Faransa, Emmanuel Macron yayin wani taro. Hoto: Emnanuel Macron.
Source: UGC

An kai kokon kawuna makabarta domin birne su

A ranar Talata kuma, an dauke su cikin kwalaye da aka lullube da tutar Madagascar, aka yi jerin gwanon mota a babban birnin har zuwa makabarta.

Shugaba Andry Rajoelina, jami’an gwamnati da kuma dattawan kabilar Sakalava sun halarci wannan bikin tarihi na dawo da kawunan kakanninsu.

Kara karanta wannan

Burkina Faso ta tsaurara doka, gwamnatin Soja ta dauki mataki a kan auren jinsi

Za a tafi da kawunan zuwa Belo Tsiribihina, wani gari da ke gabar yammacin teku, kilomita 320 daga Antananarivo, domin birne su.

A lokacin mika su a Paris, Ministan Al’adu na Faransa, Rachida Dati, ta bayyana cewa kwamitin bincike ya tabbatar da cewa kawunan na Sakalava ne.

Amma sun ce za a iya kyautata zaton cewa daya daga cikin kawunan da aka kawo na Sarki Toera ne.

Shin akwai sauran kokon kawunan sarakuna a Faransa?

Wannan mataki wani bangare ne na sabon nazari da Faransa ke yi game da tarihin mulkin mallakanta.

Kafin wannan lokaci, sai majalisa ta amince kafin a dawo da irin wadannan abubuwa.

Madagascar, wacce ta sha mulkin mallakar Faransa sama da shekaru sittin kafin samun ’yancin kai a 1960, har yanzu tana da daruruwan kawunan kakanninta a Faransa.

Faransa ta horas da jami'an NDLEA a Najeriya

Kun ji cewa gwamnatin Faransa ta tabbatar wa NDLEA tallafin horaswa, karin kwarewa da kayan aiki domin yakar ta’ammali da miyagun kwayoyi.

Laftanal Janar Regis Colcombet ya ce tattaunawar na daga cikin yarjejeniyoyin da aka cimma tsakanin shugaba Emmanuel Macron da Bola Tinubu.

Shugaban NDLEA, Janar Buba Marwa (Mai ritaya) ya bukaci karin horo kan dabarun aiki, binciken intanet da kuma fasahar zamani.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.