An Rage Mugun Iri, Jami'an DSS da Sojoji Sun Hallaka Rikakkun Ƴan Bindiga 50

An Rage Mugun Iri, Jami'an DSS da Sojoji Sun Hallaka Rikakkun Ƴan Bindiga 50

  • Rundunar jami'an farin kaya ta DSS tare da Sojojin Najeriya sun kashe yan bindiga da dama a Arewacin Najeriya
  • Akalla yan bindiga 50 aka tabbatar sun mutu a karamar hukumar Mariga da ke Jihar Niger a Arewa ta Tsakiya
  • Kakakin majalisar Jihar Niger, Abdulmalik Sarkin-Daji, ya yaba da jarumtar jami’an tsaro yana cewa sun nuna kwarewa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Minna, Niger - Al'umma da dama sun samu sauki bayan hadin gwiwar jami'an tsaro sun yi fata-fata da yan bindiga.

Hukumar DSS da rundunar sojojin Najeriya sun samu nasara a yaki da ‘yan bindiga a Niger da ke Arewa ta Tsakiyar Najeriya.

Sojoji da DSS sun hallaka yan bindiga a Niger
Rundunar sojoji da wasu miyagun yan bindiga. Hoto: HQ Nigerian Army.
Source: Twitter

An hallaka yan bindiga da dama a Niger

Rahoton Zagazola Makama shi ya tabbatar da haka a yau Laraba 27 ga watan Agustan 2025 da muke ciki.

Kara karanta wannan

Ba dadi: 'Yan bindiga sun kashe mafarauta yayin artabu a Neja

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majiyoyi sun ce harin ya yi sanadin mutuwar akalla yan bindiga 50 inda suka kubutar da wadansa aka sace.

Lamarin ya faru ne ranar 26 ga watan Agusta a kauyen Kumbashi, Mariga, inda aka ce wannan shi ne mafi nasara cikin kwanakin nan.

Kakakin majalisar Jihar Niger, Abdulmalik Mohammed Sarkin-Daji, ya bayyana aikin a matsayin wanda aka nuna fasaha yana jinjina musu.

Shaidu sun shaida cewa yan bindiga 300 dauke da manyan makamai sun yi yunkurin mamaye Kumbashi da misalin karfe 3:00.

Sai dai jami’an tsaro sun fatattake su bayan musayar wuta, inda suka kashe fiye da 50, wasu kuma sun gudu da raunuka, Vanguard ta ruwaito.

“Mutanena sun tabbatar da cewa yan bindiga sun kwashe gawarwakin abokanansu, suka saka a buhuna sannan suka dauke su da babura."

- In ji Sarkin-Daji

Kakakin majalisar, wanda ke wakiltar Mariga, ya kara da cewa an ceto mutum bakwai, tare da dawo da shanun da aka sace daga barayin.

Kara karanta wannan

Tura ta kai bango: 'Yan majalisar PDP sun taso Tinubu a gaba kan tsadar rayuwa

An hallaka yan bindiga 50 a Niger
Taswirar jihar Niger da ke Arewa ta Tsakiya Najeriya. Hoto: Legit.
Source: Original

Yadda aka cafke hatsabibin dan bindiga

Wannan ya biyo bayan nasarar hukumar DSS a Wawa, inda aka kama Abubakar Abba, shugaban kungiyar Mahmuda, daya daga cikin kungiyoyin ta’addan da aka fi tsoro.

A cewar mazauna yankin, wannan nasara ta kara musu kwarin gwiwa, ganin jami’an tsaro sun fafata da makiyaya masu rinjaye sau shida.

“Sun tsaya tsayin daka duk da cewa daruruwan yan bindiga sun kewaye su, da jarumtarsu, Kumbashi ya tsira."

- Cewar wani mazaunin gari.

Sarkin-Daji ya yi kira ga al’ummar jihar su ci gaba da ba da bayanai ga jami’an tsaro domin ci gaba da murkushe kungiyoyin miyagun.

Ya kuma tabbatar da cewa majalisar za ta ci gaba da tallafawa tsare-tsare na tsaro don tabbatar da zaman lafiya a fadin jihar Niger.

Sojoji sun kashe yan bindiga a Sokoto

Mun ba ku labarin cewa dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar hallaka wasu 'yan ta'adda na kungiyar Lakurawa a jihar Sokoto.

Kara karanta wannan

'Kowa ya shirya,' Ana fargabar ambaliya za ta shafi yankuna 14 a jihohin Arewa 9

Sojojin sun yi wa 'yan ta'addan kwanton bauna ne a karamar hukumar Tangaza lokacin da suka je sayen kayan abincin da za su yi amfani da su.

Karamar hukumar Tangaza na daga cikin wuraren da 'yan ta'addan Lakurawa suke addaba da kai hare-haren ta'addanci a jihohin Sokoto da Kebbi.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.