ADC: An Samu Wanda Zai Dawo da Tallafin Man Fetur idan Ya Zama Shugaban Kasa a 2027

ADC: An Samu Wanda Zai Dawo da Tallafin Man Fetur idan Ya Zama Shugaban Kasa a 2027

  • Tsohon dan takarar shugaban kasa a inuwar ADC, Dumebi Kachikwu ya ce bai kamata a cire tallafin man fetur a Najeriya ba
  • Kachikwu ya ce kamata ya yi gwamnati ta zakulo masu karkatar da kudin tallafin, ta hukunta su maimakon laifinsu ya shafi talakawa
  • Ya kuma musanta batun cewa Bola Tinubu ya cire tallafin man fetur, yana mai cewa tun asali babu tanadin shi a kasafin kudi

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - 'Dan takarar shugaban kasa na ADC a zaben 2023, Dumebi Kachikwu, ya bayyana cewa jam’iyyar ba za ta lamunci wasu tsofaffin ‘yan siyasa su shigo su kwace iko ba.

Kachikwu ya kuma jaddada cewa zai sake neman takarar shugaban kasa a zabe mai zuwa, yana mai cewa bai kamata wani dan Arewa ya nemi takara a 2027 ba.

Kara karanta wannan

Gudaji Kazaure da manyan ƴan siyasa 7 da suka hango faduwar Tinubu da APC a 2027

Dumebi Kachikwu.
Hoton Dumebi Kachikwu, tsohon dan takarar shugaban kasa a inuwar ADC Hoto: Dumebi Kachikwu
Source: Facebook

Mista Dumebi Kachikwu ya yi wannan furucin ne a wata hira da aka yi da shi a baya-bayan nan, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

'Dan takaran ADC ya gargadi Atiku Abubakar

Ya ce wasu ‘yan siyasa sun hada kai domin kwace jam’iyyar ADC daga hannun wadanda suka sha wahala wajen gina ta, don cimma burinsu na shugabanci a zaben 2027.

Kachikwu ya ce ADC na nan kan manufofinta na bayar da dama ga sababbin fuska, ba wai ga wadanda suka riga suka samu dama amma suka kasa ceto Najeriya daga talauci da matsalolin tattalin arziki ba.

“Ina gargadin duk wani dan takarar da yake son amfani da ADC, musamman Atiku Abubakar, ya hakura. Ya kamata Atiku ya koma ya huta. Mun taba ba shi dama a baya amma bai yi abin da ake bukata ba.”

An nemi 'yan Arewa su hakura da takara a 2027

Da yake magana kan zaben 2027, Kachikwu ya ce kowa na da ‘yancin tsayawa takara, amma ya kamata a ba yankin Kudu dama kamar yadda Arewa ta samu a baya.

Kara karanta wannan

Tinubu ya magantu daga Japan, ya fadi abin da ba a sani ba game da gwamnatinsa

“Idan akwai wanda zai kalubalanci shugaban kasa mai ci, Bola Tinubu, to ya kamata ya fito daga Kudu. Wannan shi ne adalci da rikon amana a tsarin siyasar Najeriya,” inji shi.

Kachikwu ya sha alwashin dawo da tallafin fetur

Game da batun tallafin fetur, Kachikwu ya yi bayanin cewa idan ya zama shugaban kasa zai dawo da tallafin mai domin 'yan kasa su amfana, rahoton Politics Nigeria.

“A ganina ya kamata kowace kasa mai arzikin man fetur ta bayar da tallafi ga jama’arta. Ba daidai ba ne talakawa su ci gaba da wahala saboda rashin iya tafiyar da tsarin tallafi.
"Abin da ya kamata mu yi shi ne gurfanar da wadanda suke wawure kudin da ake warewa don tallafin mai, ba wai a dauke tallafin gaba daya ba," in ji shi.
Tsohon dan takarar ADC, Dumebi Kachikwu.
Kachikwu ya yi ikirarin cewa zai dawo da tallafin mai a Najeriya Hoto: Dumebi Kachikwu
Source: Twitter

Kachikwu ya ce bai kamata a dora laifin cire tallafin fetur a kan Tinubu ba, domin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ne bai tanadi kudin tallafi a kasafin kudi ba.

Kachikwu ya soki hadakar 'yan adawa a ADC

A wani labarin, kun ji cewa Dumebi Kachikwu ya yi zargin cewa haɗakar ƴan adawa shiri ne domin cika burin tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar.

Kara karanta wannan

Sheikh Daurawa ya jero abubuwa 7 da za su karawa mace daraja

Ya yi ikirarin cewa haɗakar ƴan adawa da ta rungumi ADC a matsayin jam'iyyar da za ta yi amfani da ita, ta gama tsara wanda za ta ba tikitin takara a 2027.

Kachikwu ya kuma yi zargin cewa Peter Obi na shirin barin ƙawancen domin ya bi wata hanya wajen cimma burinsa na takarar shugaban ƙasa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262