Bayanai Sun Kara Fitowa daga EFCC, An Ji Gaskiyar Dalilin Neman Surukin Atiku Ruwa a Jallo

Bayanai Sun Kara Fitowa daga EFCC, An Ji Gaskiyar Dalilin Neman Surukin Atiku Ruwa a Jallo

  • Ana zargin EFCC ta ayyana neman surukin Atiku, Abdullahi Bashir Haske ne saboda dangantakarsa da tsohon mataimakin shugaban kasa
  • Mai magana da yawun hukumar EFCC ta kasa, Dele Oyewale ya musanta wannan zargi, yana mai cewa sun jima suna binciken Bashir Haske
  • Oyewale ya ce EFCC ta dauki matakin ayyana nemam surukin Atiku ne bayan ya karya sharuddan belin da aka ba shi a baya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Hukumar yaki da cin hanci da rashawa (EFCC) ta yi karin haske kan dalilin da ya sa ta ayyana neman Abdullahi Bashir Haske, ɗan kasuwa kuma surukin jagoran adawar Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar.

EFCC ta yi watsi da zargin da wasu ke yi cewa ta ayyana neman Bashir Haske ne saboda dangantakarsa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku.

Kara karanta wannan

Hafsan hafsoshi ya bukaci 'yan Najeriya su dauki makamai? Hedkwatar tsaro ta yi bayani

Abdullahi Bashir Haske.
Hoton surukin Atiki da hukumar EFCC ke nema ruwa a jallo Hoto: @OfficialEFCC
Source: Twitter

Mai magana da yawun EFCC na kasa, Dele Oyewale ne ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da wakilin jaridar Daiy Trust ranar Juma'a, 22 ga watan Agusta, 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Atiku Abubakar na cikin jagororin adawa da ake ganin suna da niyyar tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027.

Me yasa EFCC ke neman surukin Atiku?

A hirar da aka yi da shi ta wayar tarho, Dele Oyewale, ya kira wannan zargin na cewa saboda Atiku EFCC ke farautar Bashir Haske, da “zargi mara amfani."

Ya bayyana cewa hukumar EFCC ta dauki tsawon shekaru ta na binciken Bashir Haske, kuma yana kan beli ne amma ya karya sharuddan belin.

Oyewale ya ce:

"Abdullahi Bashir Haske mutum ne da muka dade muna bincike a kansa. Mun ba shi beli amma ya karya sharuddan belin, shi ya sa muka ayyana nemansa ruwa a jallo. Ta yaya wani zai yi irin wannan zargi?’”

Kara karanta wannan

Ana wata ga wata: Shugaban Boko Haram, Bakura ya karyata labarin kashe shi

Yadda EFCC ta ayyana neman surukin Atiku

Hukumar ta EFCC ta fitar da sanarwa a daren Alhamis inda ta bayyana cewa tana neman surukin Atiku kan zargin haɗin baki wajen aikata laifi da kuma safarar kudin haram.

A sanarwar da EFCC ta wallafa a X, ta roƙi jama’a su taimaka da bayanai kan inda Abdullahi Bashir Haske yake ta hanyar kai rahoto ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa ko wani daga cikin ofisoshin EFCC.

Abdul'ahi Bashir Haske.
Hoton matashin dan kasuwa kuma surukin Atiku, Abdul'ahi Bashir Haske a wurin taro Hoto: @jonahkingsley13
Source: Twitter

Hukumar ta kuma bukaci ‘yan Najeriya su bayar da sahihan bayanai ta ofisoshinta da ke manyan birane kamar Ibadan, Uyo, Sokoto, Maiduguri, Benin, Makurdi, Kaduna, Ilorin, Enugu, Kano, Lagos, Gombe, Fatakwal da Abuja.

Wannan lamari dai ya tayar da kura a Najeriya, inda aka fara zargin EFCC na neman taba Atiku ne ta hanyar surukinsa, zargin da hukumar ta musanta.

EFCC ta tsare wasu jami'an hukumar NAHCON

A wani labarin, kun ji cewa hukumar EFCC ta tsare manyan jami’an hukumar NAHCON ta kasa bisa zargin almundahana da ta shafi aikin Hajjin bara.

Kara karanta wannan

Fadar shugaban kasa ta ragargaji Atiku, El Rufa'i kan wata nasarar da Tinubu ya samu

Rahotanni daga majiyoyin cikin jami'an EFCC sun tabbatar da cewa wadanda aka kama suna tsare a hannun hukumar EFCC tun kwanakin baya.

An tattaro cewa EFCC ta bukaci jami’an da su dawo da kuɗin da ake zargin sun amsa, amma suka ki yin hakan, abin da ya sa aka ci gaba da tsare su.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262