Mutuwa Ta Ratsa Masana'antar Fim, Firaccen Jarumi Ya Yi Bankwana da Duniya

Mutuwa Ta Ratsa Masana'antar Fim, Firaccen Jarumi Ya Yi Bankwana da Duniya

  • Masana'antar shirya fina-finai ta Nollywood ta sake yin babban rashin fitaccen jaruminta da ya ba da gudunmawa na shekaru
  • Shahararren ɗan wasan kwaikwayo na Nollywood, Fabian Adibie, ya rasu yana da shekara 82 a duniya bayan ya yi fama da jinya
  • Shugaban Best of Nollywood, Seun Oloketuyi ya tabbatar da mutuwarsa a safiyar Laraba, inda ya ce ya rasu ƙarfe 2:30 na dare

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ikeja, Lagos - An shiga jimami bayan sanar da mutuwar fitaccen jarumin fina-finai a Najeriya wanda ya ba da gudunmawa sosai.

Shahararren ɗan wasan a masana'antar Nollywood, Fabian Adibie ya rasu yana da shekara 82 a duniya bayan fama da jinya na tsawon lokaci.

Jarumin fim ya riga mu gidan gaskiya
Jarumi Fabian Adibie ya ba masana'antar Nollywood gudunmawa sosai. Hoto: Chioma Okoye.
Source: Facebook

An sanar da mutuwar jarumin fim a Najeriya

Kara karanta wannan

Lokaci ya yi: Jakadan Najeriya ya rasu a lokacin da ba a yi tsammani ba

Labarin mutuwarsa ya tabbata ne a safiyar ranar Laraba daga bakin shugaban Best of Nollywood (BON), Seun Oloketuyi wanda ya wallafa a shafin Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Seun Oloketuyi ya tabbatar da cewa marigayin ya rasu ƙarfe 2:30 na dare ranar Laraba 20 ga watan Agustan 2025 da muke ciki.

Mutuwar dattijon ta yi matukar taba mutane da dama musamman abokan aikinsa a masana'antar Nollywood duba da irin girman da yake da shi a idonsu.

A cikin gajeren rubutun da ya yi, Seun Oloketuyi ya ce:

"Jarumi a shirin 'Things Fall Apart', Fabian Adibie ya rasu, jarumin ya bar duniya da misalin karfe 2:30 na daren ranar Laraba. Karin bayani na biyo baya."

Gudunmawar marigayin a masana'antar shirya fim

Adibie ya yi fice wajen fitowa a fina-finan Nollywood na gargajiya, inda ya zama ɗaya daga cikin fitattun jaruman da ake darajawa a masana’antar.

An fi sanin jarumin da rawar da ya taka a fim ɗin “Things Fall Apart,” wani littafi na marubuci, Chinua Achebe.

An yi rashin shahararren jarumin fim a Najeriya
Mutane su yi jimamin rasuwar jarumin fim, Fabian Adibie. Hoto: Chioma Okoye.
Source: Facebook

Rudani da abokan aikin marigayin suka shiga

Tun bayan rasuwarsa, abokan aikinsa a masana'antar Nollywood da masoya sun rika aiko da sakwannin ta’aziyya ga iyalansa da kuma abokan arziki.

Kara karanta wannan

Kashim: Wike ya fallasa dalilin da ya sa Babachir Lawan ke yawan sukar Bola Tinubu

An fahimci cewa wasu sun yi jimamin rasuwarsa inda suka bayyana shi a matsayin wanda ya ba da gudunmawa a masana'antar.

Mutane da dama sun yi martani bayan sanar da rasuwar marigayin inda suke ta yi masa fatan samun rahama a gobe kiyama.

Daga cikinsu akwai wadansa suka yaba da yadda ya ba tsaya tsayin daka domin ganin an samu ci gaba a masana'antar.Nollywood saboda kwarewar da yake da shi.

Shahararren jarumin Nollywood ya bar duniya

A baya, mun ba ku labarin cewa jarumin masana'antar shirya fina-finan Nollywood, Olusegun Akinremi da aka fi sani da Cif Kanran ya mutu yana da shekaru 70 a duniya.

An tabbatar da cewa jarumin wanda ya shahara wajen fitowa a matsayin Sarki ko mai mulki ya rasu ne da safiyar ranar Juma'a 15 ga watan Agustan 2025.

A shekarun baya, Cif Kanran ya bayyana cewa ya ja baya daga shiga harkar shirin fina-finai saboda wasu matsaloli da yake fuskanta.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.