Daga ƙarshe, An Ƙwamushe Ɗan Wanda Ya Kafa Boko Haram, Marigayi Mohammed Yusuf

Daga ƙarshe, An Ƙwamushe Ɗan Wanda Ya Kafa Boko Haram, Marigayi Mohammed Yusuf

  • Hukumar tsaro ta Najeriya ta taimakawa kasar Chadi wurin tabbatar da kama wasu hatsabiban yan ta'adda
  • Sojojin Chadi sun kama ɗan marigayi Mohammed Yusuf, wanda shi ne ya kafa kungiyar Boko Haram a Najeriya
  • An kama matashin mai shekaru 18 tare da wasu biyar da ake zargi suna da alaƙa da ISWAP a wani samame

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Njamena, Chad - Hukumomi a kasar Chadi sun kama wani matashi ɗan marigayi Mohammed Yusuf, wanda ya kafa kungiyar Boko Haram.

Wannan nasara ta kama matashin mai shekaru 18 ta afku ne bayan samun bayanan sirri daga rundunar sojojin Najeriya.

Sojojin Najeriya sun taimaka an kama dan Mohammed Yusuf
Ministan tsaro, Mohammed Badaru Abubakar yayin taro da manema labarai a Abuja. Hoto: HQ Nigerian Army.
Source: Facebook

An cafke dan marigayi Mohammed Yusuf a Chadi

Rahoton Zagazola Makama ya ce kasar Chadi ba ta san matashin da sanin asalinsa ba, sai da Najeriya ta sanar da ita.

Kara karanta wannan

Fitaccen dan kasuwa a Arewa kuma na kusa da marigayi Shehu Shagari ya rasu

An bayyana hakan ne ta hanyar bayanan sirri da jami’an tsaro na Najeriya suka bayar ta haɗin gwiwa na sojojin MNJTF.

Majiyoyi sun bayyana cewa an kama matashin da ya fara gabatar da kansa da suna Abdurrahman Mohammed Abdallah tare da wasu mutum biyar da ake zargi.

Sauran sun haɗa da Hassan Abdurrahman wanda ake ganin mai kula da kayayyakin tsaro ne, Abubakar Mohammed mai ɗaukar mambobi, Abubakar Ali Madou wanda ake zargin ya ke kula da makamai.

Yadda aka kama 'yan ta'adda a Chadi

Wadannan mutane an cafke su ne yayin wani samame na yaƙi da ta’addanci a Chadi.

Daga baya jami’an tsaro suka tabbatar cewa matashin da aka kama shi ne Muslim Mohammed Yusuf, kanin Habib Yusuf wanda ake kira Abu Mus’ab Al-Barnawi, shugaban ISWAP.

Hakan ya nuna cewa yana jagorantar wata ƙungiya mai mutane shida a yankin Tafkin Chadi.

Hotunan da aka samu sun nuna matashi siriri mai sanye da riga ta wasanni launin shuɗi, wanda yake kama da mahaifinsa.

Kara karanta wannan

Ana zargin sukar gwamnati ta jawo kai hari kan jigon APC, ya sha da ƙyar a Abuja

Sojoji sun kama dan shugaban Boko Haram na farko, Mohammed Yusuf
Dan shugaban Boko Haram na farko, Mohammed Yusuf da aka kama a Chadi da Hafsan tsaron Najeriya. Hoto: Janar Christopher Musa. Hoto: @ZagazOlamakama, @HQNigerianArmy/X.
Source: Twitter

Rundunar tsaro a Chadi ta tabbatar da kamun amma ba ta bayyana cikakken bayanai ba har sai da Najeriya ta shiga.

Wata majiya ta ce:

“Wannan ba kame na yau da kullum ba ne, an haife shi a Najeriya kafin tarzomar 2009, kuma yanzu yana ƙoƙarin kafa kansa a ISWAP.” .

Mutuwar Mohammed Yusuf a hannun jami'an tsaro

Sojoji sun kama Mohammed Yusuf, wanda ya kafa Boko Haram, sannan daga baya aka kashe shi a hannun ’yan sanda a Maiduguri a 2009.

Wannan ne ya tayar da rikicin Boko Haram wanda ya bazu a Najeriya da makwabtan ƙasashe, cewar Daily Trust.

Bayan rasuwarsa, ɗansa babba Habib Yusuf ya zama shugaban ISWAP, yanzu kuma ana zargin Muslim Yusuf cewa shirya shi domin ya ci gaba da aikin ta’addanci.

Illar da kamun zai iya yiwa ISWAP

Masana sun bayyana cewa wannan kamun ya jefa ISWAP cikin matsala da jawo tasgaro ta fuskar dabaru da kuma tunani.

Kara karanta wannan

Tashin hankali: Yan bindiga sun kutsa gidan Sarki da tsakar dare, sun sace ƴaƴansa

A cewar masana, kama ɗan Yusuf zai iya rage karfi wajen jawo sababbin mabiya, kuma ya nuna yadda ake ci gaba da gadon ra’ayin ta’addanci cikin iyalai.

Borno: Boko Haram sun sace Fasto

Kun ji cewa yan ta'addan ƙungiyar Boko Haram sun yi ta'asa a wani harin ta'addanci da suka kai a jihar Borno da ke yankin Arewa maso Gabas.

Miyagun ƴan ta'addan sun hallaka mutum ɗaya tare da yin awon gaba da wani limamin cocin Katolika.

Tsagerun ba su tsaya iya nan ba, sai da suka yi awon gaba da wasu matafiya bayan sun tare motocinsu a kan hanya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.