Wata Sabuwa: Soja Ya Daɓawa Ɗan Sanda Wuƙa har Lahira, Jami'an Tsaro Sun Haɗa Kai

Wata Sabuwa: Soja Ya Daɓawa Ɗan Sanda Wuƙa har Lahira, Jami'an Tsaro Sun Haɗa Kai

  • Ana zargin wani matashin soja ya daba wa ɗan sanda wuka har lahira a unguwar Mayo-Goyi, Jalingo a jihar Taraba
  • Sojan wanda bai dade da shiga aikin ba da ake kira Dauda Dedan ya aikata hakan ne ga Aaron John wanda ya yi sanadin rayuwarsa
  • Rahoton ‘yan sanda ya ce rikici tsakanin soja da mazauna ya jawo hatsaniyar da ta kai ga mutuwar ɗan sandan cikin dare

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Jalingo, Taraba - An samu tashin hankali bayan rigima ta kaure tsakanin dan sanda da kuma soja a jihar Taraba.

Ana zargin wani soja, Dauda Dedan ya daba wa ɗan sanda, Aaron John, na rundunar Taraba wuka har lahira a Jalingo.

Soja ya hallaka dan sanda a Taraba
Wani soja ya daɓawa ɗan sanda wuƙa har lahira a Taraba. Hoto: Nigeria Police Force, HQ Nigerian Army.
Source: Twitter

Jami'in hulɗa da jama’a na ‘yan sandan jihar, James Lashen, ya tabbatar da lamarin ga manema labarai a Jalingo ranar Laraba, cewar Punch.

Kara karanta wannan

Jiragen yaki sun kona 'yan bindiga kurmus suna bikin aure a dajin Zamfara

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An kashe wani dan sanda a Adamawa

Wannan dai ba shi ne karon farko ba da ake samun matsala tsakanin wasu daga cikin jami'an sojoji da 'yan sanda a Najeriya.

Ko a shekarar 2023 an samu hatsaniya tsakanin yan sanda da sojoji wanda ya yi ajalin wani daga cikin jami'an dan sanda.

Wani dan sanda ya rasa ransa yayin wani arangama tsakanin sojoji da 'yan sanda wanda ya afku a a jihar Adamawa a Arewacin Najeriya.

Rahotanni sun tabbatar da cewa hatsariniyar ta yi ajalin jami'in dan sanda mai suna Jacob Daniel wanda tuni aka ɗauki matakin da ya dace.

Yan sanda da sojoji sun hada kai bayan rigima tsakanin jami'ansu
Ana farautar soja da ya hallaka dan sanda a Taraba. Hoto: Legit.
Source: Original

Yadda soja ya hallaka dan sanda a Taraba

Kakakin yan sanda, Lashen ya ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 9:00 na dare a ranar Litinin a Mayo-Goyi, wata unguwa da ke Jalingo.

Ya bayyana cewa marigayi John ya samu kiran gaggawa daga mazauna yankin kan wata takaddama tsakaninsu da sojan, inda ya shiga tsakani aka daba masa wuka.

Kara karanta wannan

Yaki zai kare: Bello Turji ya ajiye makamai bayan haduwa da malaman Musulunci

Lashen ya bayyana cewa sojan ya tsere bayan lamarin, kuma rundunar soji ta fara bincike don gano inda yake domin hukunta shi, Sahara Reporters ta tabbatar da batun.

Ya ce:

"Muna da tabbacin cewa rundunar soji za ta kamo sojan da ya tsere domin ya fuskanci cikakken hukunci.
"Muna aiki tare da rundunar soji, mun je gidan sojan domin tabbatar da kama shi domin ya fuskanci hukunci daidai da abin da ya aikata."

Lashen ya jaddada cewa dangantakar da ke tsakanin sojoji da ‘yan sanda a jihar na da kyau kuma suna ci gaba da aiki tare.

Sojoji sun daku da 'yan sanda a Delta

A baya, mun ba ku labarin cewa rundunar sojin saman Najeriya ta bayyana cewa ta dauki mataki kan rikicin da ya faru tsakanin wasu jami’anta da ‘yan sanda a jihar Delta.

Jami’in hulda da jama’an sojojin, AVM Olusola Akinboyewa, ya ce an dauki matakan da suka dace don inganta fahimtar juna tsakanin jami’an tsaro.

An tabbatar da cewa an kula da ‘yan sandan da suka jikkata yayin da jami’an tsaron da suka yi hannun riga ke fuskantar hukunci bisa ka’idojin soja.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.