Yadda Masu Zuba Jari daga Ƙasashen Duniya Suka 'Kunyata' Kano, Gombe da Jihohi 30 a Najeriya

Yadda Masu Zuba Jari daga Ƙasashen Duniya Suka 'Kunyata' Kano, Gombe da Jihohi 30 a Najeriya

  • Najeriya ta samu ƙarin zuba jari a fannoni daban-daban a shekarar 2024 idan aka kwatanta da adadin jarin da aka zuba a 2023
  • Sai dai duk da wannan ci gaba da aka samu, masu zuba jari daga ƙasashen ƙetare sun kaucewa jihohi 32 a Najeriya a bara
  • Daga cikin waɗannan jihohin da ba su samu masu ziba jari ba a 2024 har da Kano, Katsina, Bauchi da dai wasunsu a sassan ƙasar nan

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Ƴan kasuwa daga kasashen ƙetare da ke shigowa Najeriya suna zuba hannun jari sun ƙauracewa jihohi 32 a sheƙarar 2024.

Alƙaluma sun nuna cewa masu zuba jari daga ƙasashen waje sun yi watsi da jihohi 32 a Najeriya a shekarar 2024, duk da cewa an samu ƙarin zuba jari a wannan shekara.

Kara karanta wannan

Ana murnar Bello Turji ya miƙa wuya, ƴan bindiga sun tarfa mutane 150 a Zamfara

Masu zuba jari daga ƙasashen ketare.
Masu zuba jari daga ƙasashen waje sun kauracewa jihohi 32 a shekarar 2024 Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

An samu karin zuba jari a Najeriya a 2024

Jaridar The Cable ta tattaro cewa a 2024, darajar hannun jarin da ƴan ƙasashen ƙetare suka zuba a Najeriya ya ƙaru da kashi 215%, daga Dala biliyan 3.91 a 2023 zuwa Dala biliyan 12.32 a 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wannan na ƙunshe ne a cikin rahoton “Jarin da ya shigo Najeriya” na farkon kwata (Q1) na shekarar 2025 da Hukumar Kididdiga ta Ƙasa (NBS) ta fitar a ranar Talata.

Jarin waje na nufin kuɗaɗen da ke shigowa ƙasa daga ƙetare domin zuba jari a fannoni kamar kasuwanci, masana’antu da ayyukan kuɗi.

Jerin jihohi 32 da masu zuba jari suka ƙaurace

A cewar rahoton, jihohi 32 da masu zuba jari suka kau da kansu daga gare su sun haɗa da:

1. Jihar Abia

2. Jihar Adamawa

3. Jihar Akwa Ibom

4. Jihar Anambra

5. Jihar Bauchi

6. Jihar Bayelsa

7. Jihar Benuwai

Kara karanta wannan

APC ta yi wa Tinubu alkawari yayin da ta jaddada mubaya'a ga Ganduje a Kano

8. Jihar Borno

9. Jihar Kuros Riba

10. Jihar Delta

11. Jihar Ebonyi

12. Jihar Edo

13. Jihar Enugu

14. Jihar Gombe

15. Jihar Imo

16. Jihar Jigawa

17. Jihar Kano

18. Jihar Katsina

19. Jihar Kebbi

20 Jihar Kogi

21. Jihar Kwara

22. Jihar Nasarawa

23. Jihar Neja

24. Jihar Ogun

25. Jihar Ondo

26. Jihar Osun

27. Jihar Filato

28. Jihar Ribas

29. Jihar Sakkwato

30. Jihar Taraba

31. Jihar Yobe

32. Jihar Zamfara.

Jihohi 8 da ba a zuba jari ba a shekara 6

Bincike ya kuma nuna cewa jihohi takwas daga cikin waɗannan 32 ba su samu ko kwabo daga jarin waje ba tsawon shekaru shida da suka gabata, wato daga 2019 zuwa 2024.

Jihohin su ne, Bayelsa, Ebonyi, Gombe, Jigawa, Kebbi, Taraba, Yobe da kuma Zamfara.

Wannan na nuna irin ƙalubalen da wasu yankuna ke fuskanta wajen jawo hankalin masu zuba jari daga ƙasashen waje.

Kara karanta wannan

Shugabanin ADC a jihohi sun shirya tumbotsai, za su jawo matsala ga tafiyar 2027

Ɗangote zai sayar da hannun jari ga ƴan Najeriya

A wani rahoton, kun ji cewa hamshaƙin attajirin nan, Alhaji Aliko Ɗangote ya bayyana shirinsa na bai wa ƴan Najeriya damar mallakar hannun jari a matatarsa.

Ya bayyana cewa matatar tana samar da tan 2,500 na iskar gas a rana domin bunkasa amfani da makamashi wajen girki a gidaje.

Dangote ya ce shirye yake ya hada gwiwa da gwamnatoci, 'yan kasuwa masu zaman kansu da cibiyoyi domin ciyar da harkar man fetur gaba a nahiyar Afirka.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

iiq_pixel