Za a Sheka Ruwan Sama a Kano, Kaduna, NiMET Ta Hango Ambaliya a Jihohi 3

Za a Sheka Ruwan Sama a Kano, Kaduna, NiMET Ta Hango Ambaliya a Jihohi 3

  • Hukumar NIMET ta ce za a samu ruwan sama da tsawa a jihohin Arewa kamar Adamawa, Taraba, Jigawa da Bauchi a safiyar Talata
  • Da yamma kuma, za a yi ruwan sama a Gombe, Zamfara, Borno, Kaduna da Kano, wanda zai iya daukar lokaci mai tsawo
  • NIMET ta yi gargadin ambaliya na iya faruwa a Bauchi, Kaduna da Plateau, ta bukaci jama’a su dauki matakan kariya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

FCT, Abuja - Hukumar hasashen yanayi a Najeriya, NIMET ta yi bayani kan hasashen yau Talata a Najeriya.

Hukumar NIMET ta ce za a sheka ruwan sama a wasu jihohin Arewa da ta ce akwai fargabar samun ambaliyar ruwa.

NIMET ta ce za a sheka ruwan sama a jihohin Arewa
NIMET ta yi hasashen sheka ruwan sama a jihohin Adamawa, Taraba. Hoto: NIMET Nigeria.
Source: UGC

Ruwan sama: Hasashen NIMET a yau Talata

Hakan na cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a daren jiya Litinin 4 ga watan Agustan 2025 a shafinta na X.

Kara karanta wannan

Ruwa zai yanke: NiMet ta saki sunayen jihohi 6 da za su fuskanci fari a Agusta

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

NIMET ta ce da safiyar yau Talata 5 ga watan Agustan 2025 za a samu tsawa da ruwan sama matsakaici a Adamawa.

Sauran jihohin da hukumar da jero sun hada da Taraba, Bauchi, Jigawa, Kano da kuma jihar Kaduna da ke Arewa maso Yamma.

Fargabar samun ambaliya a wasu jihohi

Har ila yau, Hukumar ta ce a yammacin yau Talata za a samu matsakaicin ruwan sama da kuma tsawa a wasu jihohin Arewacin Najeriya.

Jihohin sun hada da Gombe, Bauchi, Zamfara Kaduna, Kano da kuma Borno wanda zai dauki wani lokaci.

Sai dai kuma hukumar ta yi gargadin za a iya samun ambaliyar ruwa a jihohin Bauchi da Kaduna da kuma Plateau.

An yi hasashen samun ruwan sama a Kano da Kaduna
NIMET ta yi hasashen ruwan sama a Kano da Kaduna da Gombe. Hoto: Legit.
Source: Original

Hasashen ruwan sama a Abuja da Nasarawa

Bugu da kari, NIMET ta bayyana a yankin Area ta Tsakiyar Najeriya, za a samu matsakaicin ruwa a jihohin Niger da Kogi.

Sannan birnin Abuja zai samu ruwa, sai kuma Nasarawa da Kwara da Plateau da kuma jihar Niger.

Kara karanta wannan

Akwai matsala: Adamawa da jihohi 7 za su fuskanci ambaliya daga Litinin zuwa Laraba

Wannan hasashen ya biyo bayan shiga watan Agusta da ake yawan samun ruwa a kai a kai ba tare da kakkautawa ba.

Hukumar NiMET ta ce da safiyar Talata za a samu ruwa a jihohin Kudancin Najeriya da suka hada da Enugu da Edo.

Sauran sun hada da Ondo da Anambra da Cross Rivers, Rivers da kuma jihar Delta a Kudu maso Kudancin kasar.

Sai dai hukumar ta ce za a iya fuskantar ambaliya a jihohin Lagos, Oyo, Ogun, Akwa Ibom, Bayelsa.

Sai kuma jihohin Cross River da Delta inda ta shawarci alumma da su dauki matakan kariya kan abin da ka iya biyo baya.

NiMET ta fitar da hasashen wata Agusta

Kun ji cewa hukumar NiMet ta bayyana cewa ruwan sama da ya wuce kima zai sauka a jihohin Arewa 10 da suka hada da Sokoto, Zamfara a watan Agusta.

Hukumar ta ce za a samu saukin ruwa a Arewa ta Tsakiya, NiMet ta ce akwai yiwuwar jihohin Kudu maso Yamma su fuskanci fari.

Ta ba jama’a shawara da hukumomi da su shirya don tunkarar ambaliya, cututtuka da sauran abubuwan da ruwan Agusta zai zo da su.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.