'Sau 3 Muna Zama da Turji a Wata 1': Shehin Malami Ya Ja Hankalin Hukumomi kan Sulhu

'Sau 3 Muna Zama da Turji a Wata 1': Shehin Malami Ya Ja Hankalin Hukumomi kan Sulhu

  • Musa Yusuf Assadus Sunnah ya sake bayyana damuwarsa kan ta'addanci, yana cewa matsalar Arewa maso Yamma ta yi tsanani fiye da yadda ake tsammani
  • Ya ce sun ziyarci Bello Turji sau uku a watan da ya wuce domin zaman sulhu, inda suka fuskanci haɗari don ceto al’umma daga bala’i
  • Malamin ya koka kan yadda wasu ke sukar kokarinsu, duk da suna shiga hatsari suna wa'azi da rokon 'yan bindiga da su ji tsoron Allah

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kaduna - Sheikh Musa Yusuf Assadus Sunnah ya sake yin magana kan ta'addanci da ke faruwa musamman a Arewa maso Yamma.

Sheikh Assadus Sunnah ya ce tabbas akwai matsala musamman game da abubuwan da suke gani.

Sheikh ya fadi abin da suka fadawa Bello Turji
Sheikh Assadus Sunnah ya ce sun yi zama sau da yawa da Bello Turji. Hoto: Sheikh Musa Yusuf Assadus Sunnah.
Source: Facebook

Sheikh Assadus Sunnah ya sake magana kan ta'addanci

Malamin ya bayyana haka a cikin wani bidiyo yayin karatu na musamman kan tsaro a shafinsa na Facebook.

Kara karanta wannan

Musulmi sun fusata da dodanni suka farmaki limamin Musulunci, an roki gwamna

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cikin bidiyon, malamin ya ce idan har ya bayyana irin karfin da yan bindiga suke da shi mutane za su yi mamaki.

Ya kara jaddada muhimmancin sulhu da yan bindiga duba da abin da ke faruwa musamman ma rasa rayuka.

Ya ce:

"Alhamdulillahi muka tashi muka tafi karkashin wannan kwamitin domin zaman sulhu.
"Da yawa idan na ce na je na gano Turji ido da ido mamaki ma yake, a cikin watan nan da ya wuce sau uku muna zuwa.
"Kamar yadda muke zaune da kai haka, ta ganin Annabin tsohuwa kuru-kuru gani ga shi yana gani na ina ganinsa.
"Kuma mun tashi a gabansa mun fada masa a ji tsoron Allah akwai abubuwan da ake yi wadanda ba daidai ba ne."
Sheikh ya sake magana kan sulhu da su Bello Turji
Sheikh Assadus Sunnah ya bukaci sulhu da su Bello Turji. Hoto: Sheikh Musa Yusuf Assadus Sunnah.
Source: Facebook

Abin da Assadus Sunnah suka fadawa Bello Turji

Sheikh Musa Assadus Sunnah ya ce a matsayinsu na malamai sun fadawa Bello Turji da sauran yan uwansa gaskiya kan abin da ke faruwa.

Kara karanta wannan

Shugaban Iran ya gargaɗi Tinubu kan tsoma baki a rikici da Isra'ila? An samu bayanai

Ya ce sun yi musu wa'azi kan cewa su ji tsoron Allah kan abubuwan da suke yi saboda akwai kura-kurai a ciki.

Ya kara da cewa:

"Sun yi magana,'mun yi magana, sun fadi dalilansu, duk wanda ya ke ji shi namiji ne ya zo mu dauke shi ya je can a gabansu ya ce musu su ji tsoron Allah."

Malamin ya bayyana hatsarin da suka shiga duk domin ceto al'umma daga bala'in da ta shiga amma wasu na sukarsu.

Shehin ya koka kan wasu da ke zaune a cikin gari ba su san komai ba sai dai su dura muku zagi yayin da kuke ƙoƙarin ceto al'umma.

Turji: Shinkafi ya magantu kan matsalar tsaro

Kun ji cewa mai sharhi kan matsalar tsaro, Sani Shinkafi ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta dakile rundunar CJTF da CPG daga kashe Bello Turji a Zamfara.

Shinkafi ya ce CJTF da CPG na dab da shafe babin Turji, gwamnatin tarayya ta ce su koma Shinkafi.

A cewarsa, gwamnatin tarayyar ta ce za ta yi sulhu da shugaban ƴan ta'addar, abin da Bello Turji ya ƙi amincewa da shi.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.