Musulmi Sun Fusata da Dodon Gargajiya Ya Farmaki Limamin Musulunci, an Roki Gwamna

Musulmi Sun Fusata da Dodon Gargajiya Ya Farmaki Limamin Musulunci, an Roki Gwamna

  • Wani dodon gargajiya ya kai hari ga wani Liman a Ogbomoso, inda ya cire masa hula yayin da yake kan babur
  • Kungiyar Muslim Public Affairs Centre (MPAC) ta ce hakan saba wa doka ne kuma gwamnati ta binciki Lobanika da dukan masu hannu
  • MPAC ta bukaci a daina amfani da bukukuwan gargajiya wajen tauye hakkin jama’a da takura musu

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ogbomoso, Oyo - Kungiyar Muslim Public Affairs Centre (MPAC) ta nuna takaici kan kai hari da aka kai kan liman.

Kungiyar ta bayyana takaicinta kan harin da wani dodon gargajiya mai suna Lobanika ya kai wa wani Liman a Ogbomoso a jihar Oyo.

An farmaki limamin Musulunci a Oyo
Musulmi sun bukaci adalci bayan dodon gargajiya ya farmaki liman a Oyo. Hoto: Seyi Makinde.
Source: Facebook

Cin zarafin da aka yiwa limamin Musulunci

Daily Trust ta ce lamarin ya faru a kwanakin baya a Oja'gbo, Ogbomoso, inda dodon ya cire hular Liman yayin da yake kan babur ba tare da wani dalili ba.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kai mummunan farmaki kan manoma a Sokoto, an samu asarar rayuka

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An bayyana dodon da cewa yana da ɗabi’ar tashin hankali, inda har ya dawo baya domin ganin yadda Liman ɗin zai mayar da martani.

Shugaban Limaman Ogbomoso, Sheikh Teliat Ayilara da wasu malaman addini sun bayyana abin da ya faru a matsayin cin zarafi da rashin mutunci.

MPAC ta bayyana cewa irin wannan cin zarafi ya nuna yadda wasu ke raina hakkin bil’adama da dokar kasa cikin girman kai.

Kungiyar Musulmi ta soki dodon da ya kai hari kan liman
Musulmi sun yi bukaci adalci bayan hari kan limamin Musulunci. Hoto: Legit.
Source: Original

Hari kan liman: Abin da kungiar MPAC ta ce

Shugaban MPAC, Disu Kamor, ya ce wannan lamari yana nuna yadda wasu ke amfani da bukukuwan al’ada wajen gallaza wa mutane ba tare da hukunci ba.

Kamor ya ce sanarwar kungiyar Oloolu a Ibadan da ta haramta wa mata shiga wasu wurare da tilasta wa maza sanya sutura irin tasu, saba wa doka ne.

Ya ce babu wata kungiya, gargajiya ko addini da ke da hurumin tauye hakkin dan kasa a Najeriya kamar yancin tafiya ko sutura.

Kara karanta wannan

Jarumin fim, Don Richard ya talauce, yana neman taimakon N30m daga 'yan Najeriya

MPAC ta bukaci ‘yan sanda su binciki lamarin tare da gurfanar da Lobanika da duk wanda ke da hannu a harin da aka kai, cewar Daily Post.

Kungiyar MPAC ta roki gwamna Makinde

Kungiyar ta roki gwamnatin jihar Oyo da ta sanya doka kan bukukuwan dodannin domin kare ‘yancin jama’a da tabbatar da zaman lafiya a gari.

Ta kuma yi kira ga Musulmai da su zauna lafiya, amma ka da su dauki hakuri a matsayin rauni ko yarda da zalunci.

A cewar MPAC, Najeriya mallakin kowa ce, kuma babu wata kungiya da ta fi karfin doka.

Kungiyar ta ce za ta ci gaba da sa ido kan irin waɗannan lamura tare da goyon bayan kare martaba da hakkin Musulmai da sauran jama’a.

Ana zargin Sarki da kokarin hana Musulunci

A baya, kun ji cewa wasu masu shigar dodanni sun kai hari kan gidan limamin gari a Ondo da kuma masallacinsa, inda suka lakada wa iyalansa duka.

Kungiyar kare hakkin Musulmi ta MURIC ta soki harin, ta kira shi da barna, rashin hankali kuma abin ta da hankali tare da neman a hukunta masu laifin.

Farfesa Ishaq Akintola ya ce maimakon Sarkin ya hukunta masu laifi, sai ya ci tarar limamin da iyalinsa, tare da barazanar kora.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.