An Zo Wajen: Kamfanin NNPCL Ya Yi Magana kan Sayar da Matatar Port Harcourt

An Zo Wajen: Kamfanin NNPCL Ya Yi Magana kan Sayar da Matatar Port Harcourt

  • Kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) ya kawo karshen jita-jita dangane da batun sayar da matatar mai ta Port Harcourt da ke jihar Rivers
  • Shugaban kamfanin NNPCL, Bashir Bayo Ojulari, ya ce babu shirin sayar da matatar wacce aka dakatar da aiki da ita a kwanakin baya
  • Ya nuna tun da farko an yi kuskure wajen fara da amfani da matatar kafin a kammala gyaranta

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) ya yi magana kan sayar da matatar mai ta Port Harcourt.

Kamfanin na NNPCL ya bayyana a hukumance cewa ba zai sayar da matatar mai ta Port Harcourt ba, yana mai jaddada aniyarsa ta kammala gyaranta da kuma ci gaba da riƙe matatar.

NNPCL ba zai sayar da matatar Port Harcourt ba
Kamfanin NNPCL ya ce ba zai sayar da matatar Port Harcourt ba Hoto: @nnpclimited
Asali: Twitter

Jaridar The Punch ta ce shugaban kamfanin NNPCL, Bashir Ojulari, ne ya bayyana hakan a yayin taron tattaunawa da ma’aikata da aka gudanar a ranar Talata, 28 ga watan Yulin 2025.

Kara karanta wannan

Siyasa: Rikici ya yi kamari a SDP, an tura mutanen El Rufa'i kurkuku

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An dai gudanar da taron ne a hedkwatar kamfanin NNPCL dake birnin tarayya Abuja, rahoton tashar Channels tv ya tabbatar.

NNPCL ba zai saida matatar Port Harcourt ba

Ya bayyana cewa wannan matsayar ba sauyin ra’ayi bane, sai dai an cimma ta ne sakamakon cikakkiyar bitar da ake gudanarwa a kan matatun mai na Port Harcourt, Kaduna da Warri.

“Ina mai bayyana cewa nazarin da ake yi yanzu ya nuna cewa matakin da aka ɗauka a da na fara aiki da matatar Port Harcourt kafin a kammala cikakken gyaranta ya kasance mara kyau kuma ba ya da alfanu a kasuwanci."

- Bashir Bayo Ojulari

Duk da cewa ana samun ci gaba a kan dukkanin matatun guda uku, ya bayyana cewa bayanan da ke fitowa yanzu sun nuna cewa akwai buƙatar haɗin gwiwa da ƙwararrun abokan hulɗa a fannin fasaha domin kammala aikin gyara da kuma haɓaka ingancin matatun.

Kara karanta wannan

Za a caɓa: Gwamnatin Tinubu ta fara ɗiban matasa aiki domin rage zaman banza

Jawabin Ojulari ya samu maraba da tafi daga ɗaruruwan ma’aikatan da suka halarci taron, waɗanda suka nuna jin daɗinsu da mayar da hankali kan dabarar kasuwanci da kuma riƙe kadarorin kamfani.

Matsayar shugaban na NNPCL ta yi daidai da manufofin gwamnatin tarayya kan samar da tsaron makamashi, inda take ci gaba da nuna aniyarta na riƙe muhimman kadarorin makamashi a hannun gwamnati a yayin da ake ci gaba da aiwatar da gyare-gyare a sashen makamashi.

NNPCL ba zai sayar da matatar Port Harcurt ba
Kamfanin NNPCL ya kawo karshen jita-jita kan matatar Port Harcourt Hoto: @nnpclimited
Asali: Twitter

Karanta wasu labaran kan kamfanin NNPCL

Kamfanin NNPCL ya rage farashin fetur

A wani labarin kuma, kun ji cewa kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) ya rage farashin fetur a gidajen man da suke mallakinsa.

Kara karanta wannan

2027: APC ta tsorata da ake shirin kawo sauyi kan zaɓen shugaban ƙasa, gwamnoni

Kamfanin NNPCL ya rage farashin da ake siyar da fetur a birnin tarayya Abuja zuwa N890 a kan kowace lita.

Rage farashin dai na zuwa ne yayin da ake ci gaba da gasa tsakanin kamfanin NNPCL da matatai mai ta Dangote.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng