Mabambantan Ra’ayoyi daga Malaman Musulunci game da Yafewa Marigayi Buhari

Mabambantan Ra’ayoyi daga Malaman Musulunci game da Yafewa Marigayi Buhari

An sanar da rasuwar marigayi Muhammadu Buhari a yammacin ranar Lahadi 13 ga watan Yulin 2025 da muke ciki bayan fama da jinya.

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Marigayi tsohon shugaban kasa ya rasu ne bayan fama da doguwar jinya a birnin London da ke kasar Birtaniya.

Tinubu ya tura tawaga dauko Buhari a London
An binne gawar Buhari a gaban Tinubu a garin Daura. Hoto: Muhammadu Buhari, Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Twitter

Umarnin da Tinubu ya bada bayan rasuwar Buhari

Rasuwarsa ke da wuya Bola Tinubu ya umarci mataimakinsa, Kashim Shettima ya je ya taho da gawarsa zuwa Najeriya kamar yadda hadiminsa, Bayo Onanuga ya sanar a X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shettima ya isa London inda ya jajantawa iyalan marigayi tare da dawo da shi Najeriya domin yi masa sallar jana'aza, Punch ta ruwaito.

Daga karshe, an gudanar da sallar jana'izar marigayin a ranar Talata 15 ga watan Yulin 2025 a garin Daura da ke jihar Katsina.

Kara karanta wannan

Shugaban malamai a Izala, Sheikh Shu'aibu Ahmad ya rasu a jihar Gombe

Hayaniya da ta biyo bayan rasuwar Buhari

Sai dai abin da ya fi daukar hankali bayan rasuwar Buhari shi ne ce-ce-ku-ce da ake ta yi na cewa wasu ba su yafe masa ba.

An samu rarrabuwar kawuna yayin da wasu tun ranar da ya rasu suka ce sun yafe hakkinsu kuma suka yi masa addu'ar samun rahama.

Lamarin bai tsaya iya kan talakawa ba hatta malaman Musulunci a Arewacin Najeriya sun tattauna kan lamarin.

Legit Hausa ta duba ra'ayoyin malaman Musulunci kan maganar yafewa Buhari ko sabanin haka.

1. Sheikh Lawan Abubakar Triumph

Kusan Sheikh Triumph shi ya fara magana kan wannan lamari bayan rasuwar marigayi Muhammadu Buhari da Tijjanee Muhammad ya wallafa a Facebook.

Shehin ya ce gwara Buhari an ga ƙarshensa ya mutu cikin iyalansa an dauko shi an yi masa sallar kai ka san ya kaeshenka zai kasance.

Ya ce matar Buhari ta nema masa gafara kuma ko ba ka yafe masa ba Allah zai yafe masa, duk da Legit Hausa ba ta da tabbacin ta fadi haka.

Kara karanta wannan

2027: Bayan rasuwar Buhari, Shehu Sani ya faɗi abin da zai faru da Tinubu a zaɓe

A cewarsa:

"Manzon Allah SAW ya ce duk wanda ya ce a yafe masa aka ki yafe masa Allah zai yafe masa kai kuma da ba ka yafe shi ba kai da Allah."

Daga baya an ji cewa malamai sun nuna rashin ingancin wannan hadisi har ta kai wasu sun yi wa Sheikh Triumph raddi saboda kafa hujja da shi.

Sheikh ya yi magana kan yafewa Buhari
Sheikh Lawan Triumph ya ce Allah zai yafewa Buhari. Hoto: Sheikh Lawan Abubakar Triumph.
Source: Facebook

2.. Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa na daya daga cikin malaman da suka fara magana bayan rasuwar Muhammdu Buhari.

Sheikh Daurawa ya roki ƴan Najeriya su sanya Muhammadu Buhari a addu'o'insu kuma su yafe masa kura-kuransa.

Babban kwamandan rundunar Hisbah ta Kano ya yi wannan roko ne yayin da ake jimamin rasuwar tsohon shugaban ƙasar a Najeriya.

Malamin ya kuma roƙi jama'a su yiwa tsohon shugaban ƙasar addu'ar samun rahama a wurin Allah bayan rasuwarsa a birnin Landan.

Daurawa ya roki yan Najeriya su yafewa Buhari
Daurawa ya bukaci yi wa Buhari addu'ar samun rahama. Hoto: Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, Muhammadu Buhari.
Source: Facebook

3. Sheikh Musa Yusuf Assadus Sunnah

Sheikh Musa Yusuf Assadus Sunnah ya tayar da kura a kafofin sadarwa bayan ya yi magana game da yafewa Buhari a Najeriya wanda ya wallafa a Facebook.

Kara karanta wannan

Musulunci ya yi babban rashi, Sheikh Dalha Konduga ya rasu

Malamin ya ce ko da ba a yafewa Buhari ba Allah na iya yafe masa a cikin rahamarsa wanda wannan bayani ya jawo maganganu.

Ya ce:

"Maganar da wasu ke fada a ji ta daga baki na wai cewa idan hakki na Allah ne zai yafe, na bayi kuma sai idan bayi sun yafe, wannan maganar banza ce ba gaskiya ba ce.
"Ba Allah ba ne ya fada kuma ba manzon Allah SAW ba ne ya fada, idan haka ne ashe bai zama Allah ba kenan."
Sheikh Assadussunnah ya saba da malamai kan Buhari
Sheikh Assadussunnah ya jawo magana kan yafewa Buhari. Hoto: Sheikh Musa Yusuf Assadussunnah.
Source: Facebook

4. Sheikh Ishaq Adam Ishaq

Sheikh Ishaq Adam Ishaq ya yi jawabi mai ratsa zuciya kan rasuwar Muhammadu Buhari, inda ya bukaci shugabanni su ji tsoron Allah.

Ya soki malamai da ke cewa Allah SWT zai yafe wa Buhari duk da wasu ba su yafe masa ba, yana cewa hakan kuskure ne babba.

Baristan ya bayyana cewa Allah ba zai yafe hakkin wani mutum ba sai wanda aka zalunta ya yafe ko kuma an biya shi hakkinsa.

Martanin nasa na zuwa ne bayan Sheikh Musa Yusuf Assadus Sunnah ya fitar da bidiyo kan yafewa Buhari.

Kara karanta wannan

'Yadda matata ta hana ni sukar Buhari bayan ya mutu': Tsohon gwamna ya magantu

Sheikh ya yi bayani kan ce-ce-ku-ce game da yafewa Buhari
Sheikh Adam Ishaq ya soki wasu malamai kan yafewa Buhari. Hoto: Sheikh Ishaq Adam Ishaq.
Source: Facebook

5. Sheikh Bello Aliyu Yabo

Sheikh Bello Aliyu Yabo ya yi magana game ce-ce-ku-ce da ake ta yi bayan rasuwar marigayi Muhammadu Buhari kan yafe masa.

A cikin bidiyon, Bello Yabo ya ce ta yaya wasu malamai za su yi amfani da hadisi cewa ko ba ka yafe ba Allah zai tafe masa.

Malamin ya ce abin takaici ne kana ganin wadanda suka kwashe muku dukiya suna facaka amma ace a yafe musu.

Ya bayyana cewa su kam ba su yafe ba saboda bai cika sharudan tuba ba kafin ya bar duniya kuma sai an biya shi hakkinsa a lahira.

Bello Yabo ya yi zazzaga kan yafewa Buhari
Bello Yabo ya ce ba zai yafe zaluntarsa da aka yi ba. Hoto: Muhammadu Buhari, Sheikh Bello Aliyu Yabo.
Source: Facebook

Sheikh Pantami ya tuna alherin Buhari gare shi

Mun ba ku labarin cewa Farfesa Isa Ali Pantami ya ce ya zauna da Muhammadu Buhari na tsawon shekaru 24 kuma bai taba ganin rashin gaskiya a tare da shi ba.

Pantami ya bayyana cewa Buhari mutum ne mai gaskiya, kishin kasa da jajircewa, yana tunawa da kyawawan halayensa da sadaukarwa ga jama'a.

Ya ce maganar cewa Buhari bai kyauta ba gaskiya ba ne, ya sha samun kyaututtuka daga gare shi har guda biyu da ba zai manta ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.