Gwamna Ya Ɗauki Zafi, Ya Dakatar da Kwamishinoni 25 da Wasu Hadimai 60 a Ebonyi

Gwamna Ya Ɗauki Zafi, Ya Dakatar da Kwamishinoni 25 da Wasu Hadimai 60 a Ebonyi

  • Gwamna Francis Nwifuru ya dakatar da kwamishinoni 25, mataimaka 38 da sakatarori 22 saboda rashin halartar taron gwamnati
  • An hana duk wanda aka dakatar saka hannu a takardun gwamnati yayin da aka tura su hutu na wata guda ba tare da albashi ba
  • Yayin da gwamnan ya saki sunayen mukarraban gwamnatin da abin ya shafa, ya ja kunnen ma’aikatan jihar da su kiyaye ka’idojin aiki

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Ebonyi - Gwamna Francis Nwifuru na jihar Ebonyi ya dakatar da jami’an gwamnati 85 saboda rashin halartar wani taron gwamnati.

Waɗanda aka dakatar sun haɗa da kwamishinoni, manyan mataimaka na musamman, mataimaka na musamman, da kuma manyan sakatarori.

Gwamna Francis Nwifuru ya dakatar da mukarraban gwamnatinsa 85
Gwamnan jihar Ebonyi, Francis Nwifuru yana jawabi a wani taro. Hoto: @FrancisNwifuru
Source: Twitter

Gwamnan Ebonyi ya dakatar da mukarrabai 85

Gwamnan, a cikin wata sanarwa a daren Litinin, ya ce an dakatar da jami’an ne saboda rashin halartar wani muhimmin taron gwamnati kamar yadda Leadership ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Gwamna ya dakatar da hadiminsa, ya kori Ahmed Musa daga shugabancin hukumar EDOFEWMA

Mai magana da yawunsa, Monday Uzor, ya ruwaito cewa gwamnan ya yanke hukuncin cewa waɗanda abin ya shafa za su tafi hutun aiki na wata ɗaya ba tare da albashi ba.

Ya lissafo kwamishinoni 25, manyan mataimaka na musamman 14, mataimaka na musamman 24, da kuma manyan sakatarori 22 a matsayin waɗanda aka dakatar.

A cewar sanarwar, dakatarwar ta fara aiki nan take, kuma an hana waɗanda aka dakatar saka hannu kan duk wata takardar gwamnati a tsawon wannan lokacin.

Gwamnan Ebonyi ya kara tsauri kan ma'aikata

An umurci kwamishinonin da su miƙa mulki da dukkanin kadarori ko takardun gwamnati da ke hannunsu zuwa ga manyan sakatarorin ma'aikatunsu.

Sanarwar ta ce:

“Gwamnan jihar Ebonyi, Mai Girma Francis Ogbonna Nwifuru ya ba da umarnin cewa jami’an gwamnati da aka lissafta a ƙasa su tafi hutun aiki na wata ɗaya ba tare da albashi ba saboda rashin halartar wani muhimmin taron gwamnati.”

Kara karanta wannan

Noma: Hadimin Buhari ya goyi bayan Tinubu, ya fadi kuskuren da aka samu a zamaninsu

Jaridar Premium Times ta rahoto Uzor ya jaddada cewa gwamnan ya kasance mai tsauri kan dabi'un jami’an gwamnati da kuma jajircewa wajen yi wa al’ummar jihar Ebonyi hidima.

Kwamishinoni da hadiman da aka dakatar

Ga jerin sunayen jami’an da aka dakatar kamar yadda Malam Uzor ya aika a ƙasa:

Kwamishinoni 25 da aka dakatar

  1. Injiniya Stanley Lebechi Mbam
  2. Farfesa Leonard Uguru
  3. Dokta Mathew Nwobashi
  4. Farfesa Nwogo Obasi.
  5. Hon. Victor Chukwu
  6. Injiniya Jude Okpor
  7. Barr. Ikeuwa Omebe
  8. Hon. Chidi Onyia
  9. Cif Oguzo – Offia Nwali
  10. Dokta Ben. Uruchi Odo
  11. Dokta Donatus Ilang
  12. Dokta Mrs Ngozi Obichukwu
  13. Dokta Moses Ekuma Ikenna
  14. Cif Richard Idike
  15. Barr. Mrs. Felicia Nwankpuma
  16. Hon. Chinedu Nkah
  17. Injiniya Ogbonna Obasi Abara
  18. Mrs Nkechinyere Iyioku
  19. Injiniya Francis Ori
  20. Hon. Tochukwu Okorie
  21. Barr. Valentine Okike Uzo
  22. Cif Sunday Inyima
  23. Hon. Ogbonnaya Okorie
  24. Cif Elechi Elechi
  25. Hon. Stanley Ogbuewu

Manyan mataimaka na musamman (SSA)

  1. Hon. Bassey Chukwu
  2. Mrs. Rose Ofoke
  3. Mr. Kerian Ofoke
  4. Hon. Anthony Nwegede
  5. Hon. Onu Nwonye
  6. Mrs. Lilian Nwachkwu
  7. Mr. Fred Nwogbaga
  8. Hon. Paul Nwogha
  9. Hon. Pius Nwoga
  10. Hon. Ali Ikechukwu
  11. Hon. Nwiboko Chukwuma
  12. Mrs Esther Nwogha
  13. Barr. Caleb onwe
  14. Hon. Chinedu Awo

Kara karanta wannan

Ganduje, Hajiya Zainab da wasu mutane 86 da Tinubu ya ba manyan mukamai a 2025

Mataimaka na musamman (SA)

  1. Mr Mbam Emmanuel
  2. Tobias Ogbonna
  3. Easy Okike Uzo
  4. Obinna Oko Enyim
  5. Chima Nnachi Okoro
  6. Nwali Amechi
  7. Dr. Sabinus Nwibo
  8. Okorie Jideofor
  9. Sunday ogenyi
  10. Stanley Kamani
  11. Ikechukwu Jideofor
  12. Emeka Okpa Onwe
  13. David Aja
  14. Frank Uka
  15. John Nwangbo
  16. Ogbonna Melford Nwuruku
  17. Ifeanyi Ujebe
  18. Chima Ogbuagu
  19. Kizito Nwenyi
  20. Uwa Henry Ifeanyi
  21. Elechi Okechukwu Solomon
  22. Ibina John Ogbonna
  23. Mbam Ifeanyi D
  24. Nwigum Nonso Christian
Gwamnan jihar Ebonyi, Francis Nwifuru ya dakatar da kwamishinoni 25 da hadimai 60
Gwamna Francis Nwifuru, yayin da yake gabatar da kasafin kudi na 2025 gaban majalisar dokokin jihar Ebonyi. Hoto: @FrancisNwifuru
Source: Twitter

Manyan sakatarori (PS) da aka dakatar

  1. Dr. Lawrence Ezeogo
  2. Dr. Isioma C Arunne-Inyang
  3. Mrs Rose Ibe
  4. Mrs Ogechi Nwobasi
  5. Mrs Anwu Theresa
  6. Dr. Lynda Alo
  7. Mr Monday Nkwuda
  8. Mrs Mary Ngozi Otozi
  9. Mrs Martina Obiya
  10. Mrs Ogechi Anaso-Kalu
  11. Barr Emmanuel Onwe
  12. Mr Henry Nworie
  13. Mrs Joy Mbam
  14. Mrs Henrietta Ikechukwu Oruh
  15. Barr Peter Ede
  16. Dr. Gabriel Odo
  17. Mrs Mfon Williamson
  18. Ms Alusi Felicia
  19. Mrs Betty Uzoma
  20. Engr Chukwuma Ojeogu
  21. Barr Ikechukwu Alobu
  22. Mr Fidelis Nwankwo

Gwamna Nwifuru ya dakatar da mukarrabansa

A wani labarin, Legit Hausa ta rahoto cewa, gwamna Francis Nwifuru na jihar Ebonyi ya dakatar da kwamishinoni biyu kan zargin rashin ɗa'a da sakacin aiki.

Kara karanta wannan

Belin dilan ƙwaya: Gwamna Abba Kabir ya kafa kwamiti game da kwamishinansa a Kano

Kwamishinan yaɗa labarai da wayar da kan jama'a, Jude Chikadibia-Okpor ya bayyana hakan a sanarwar da aka rabawa manema labarai a birnin Abakaliki.

Jude ya ce Gwamna Nwifuru ya kuma dakatar da babban sakataren ma'aikatar lafiya da shugabannin hukumomi biyu na ɓangaren kiwon lafiya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com