Musulmi Sun Yi Babban Rashi a Najeriya, Sheikh AbdulKareem Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

Musulmi Sun Yi Babban Rashi a Najeriya, Sheikh AbdulKareem Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

  • Musulmi sun yi rashi da Allah ya karɓi ran babban limamin garin Oruwa, Sheikh AbdulKareem Olore a jihar Oyo
  • Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Oyo, Rt. Hon. Adebo Ogundoyin ya yi jimami tare da miƙa sakon ta'aziyyar rasuwar babban malamin na musulunci
  • Ya ce al'ummar musulmi na Oruwa sun yi babban rashi idan aka yi la'akari da irin gudummuwar da marigayin ya bayar a rayuwarsa

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Oyo - Babban limamin garin Oruwa da ke ƙaramar hukumar Ibarapa a jihar Oyo, Sheikh AbdulKareem Olore ya riga mu gidan gaskiya.

Babban malamin addinin musuluncin ya rasu ne bayan fama da gajeruwar rashin lafiya a garinsa na Oruwa da ke jihar Oyo a Kudu maso Yammacin Najeriya.

Kakakin Majalisar Oyo, Rt. Hon. Adebo Ogundoyin da Marigayi Sheikh AbdulKareem.
Babban limami, Sheikh AbdulKareem ya riga mu gidan gaskiya a jihar Oyo Hoto: @Adebo_Ogund
Source: Twitter

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Oyo, Rt. Hon. Adebo Ogundoyin, ya bayyana jimaminsa kan rasuwar babban limamin, kamar yada Tribune Nigeria ta rahoto.

Kara karanta wannan

Pantami ya sanar da mutuwar jigon PDP, ya shawarci al'umma game da jana'izarsa

Sheikh AbdulKareem Olore ya rasu

Sheikh AbdulKareem Olore ya rasu yana da shekaru 84 da haihuwa, kamar yadda bayanai suka tabbatar.

An tabbatar da rasuwarsa ne ta cikin wata sanarwar ta'aziyya da Shugaban Majalisar Dokokin Oyo, Ogundoyin ya rabawa manema labarai.

A cikin sanarwar, Rt. Hon. Ogundoyin ya bayyana marigayin a matsayin wani babban ginshiƙi, uba ga kowa, kuma jagora ga al’ummar Musulmi da ma dukkan al’ummar Eruwa.

Musulmi a Oruwa sun yu babban rashi

“Wannan babban rashi ne ga ƙasar Eruwa, da al’ummar Musulmi, kuma hakika mu da muka san Baba Sheikh AbdulKareem Olore muna daraja shi.
"Ba kawai babban limami bane, mutum ne mai ƙaunar zaman lafiya, hikima da tawali’u. Addu’o’insa, jagoranci da shawarwarinsa sun taimaka matuƙa wajen haɗin kan mutanenmu."

- In ji Rt. Hon. Adebo Ogundoyin

Ogundoyin ya tuna irin muhimmiyar rawa da marigayi Limamin ya taka wajen sasanta rikicin shugabanci da ya dade yana faruwa kan kujerar Babban Limamin Eruwa.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu zai halarci taron addu'a da Allah Ya karɓi rayuwar Mai Martaba Sarki

“Haƙurinsa da ƙwarewarsa a lokacin fitintinu sun ƙara nuna jajircewarsa wajen ganin an samu zaman lafiya da ci gaban al’umma da kuma tabbatar da martabar addinin Musulunci," in ji shi.
An rasa malamin musulunci a jihar Oyo.
Shugaban Majalisar Dokokin Oyo, Rt. Hon. Adebo Ogundoyin ya yi jimamin rasuwa limamin Oruwa Hoto: Legit.ng
Source: Original

Kakakin Majalisar Oyo ya yi ta'aziyya

Shugaban Majalisar ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, al’ummar Musulmi na Eruwa, da kuma shugabannin addinin Musulunci a yankin Ibarapa.

Ya bukaci al'umma su ƙarfafa kansu, kuma su yi koyi da kyakkyawar rayuwar da marigayin ya yi tare da ci gaba da riƙo da halayensa na zaman lafiya, hidima da ibada.

“Baba Olore ya yi rayuwa mai kyau, yana bautawa Allah da kuma hidima ga mutane. Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta masa, ya karɓi ayyukan alherinsa, ya kuma saka masa da Aljannatul Firdaus,” in ji Ogundoyin.

Sheikh Idris Abu Sumayya ya rasu

A wani rahoton, kun ji cewa Sheikh Idris Adam Kumbashi wanda aka fi sani da Abu Sumayya ya riga mu gidan gaskiya a Zaria, jihar Kaduna.

An rahoto cewa Sheikh Kumbashi ya sadaukar da rayuwarsa wajen hidimar addini, da'awa da koyarwa lokacin da yake raye.

Tuni dai aka an gudanar da jana'izar marigayin da misalin karfe 1:30 na rana a masallacin Juma'a na dan Magaji a Zaria.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262