Awujale: Yadda Basarake Ya Assasa Kafa APC, Nasarar Buhari a 2015

Awujale: Yadda Basarake Ya Assasa Kafa APC, Nasarar Buhari a 2015

  • Fasto Tunde Bakare ya tuno yadda aka kafa jam'iyyar APC har ta samu nasara a babban zaɓen shekarar 2015
  • Malamin addinin ya bayyana cewa Awujale na Ijebu, marigayi Oba Sikiru Adetona ya assasa kafa jam'iyyar APC
  • Ya bayyana cewa da ba don rawar ganin da basaraken ya taka ba, da ba a samar da jam'iyyar APC ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Legas - Fasto Tunde Bakare, babban mai kula da Cocin Global Community Citadel, ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa yadda gwamnatin sa ta shirya jana’izar marigayi Muhammadu Buhari.

Haka kuma, ya yi gagarumar jinjina ga Awujale na Ijebuland, Oba Sikiru Adetona, wanda shi ma ya rasu a rana ɗaya da marigayi Buhari.

Awujale ya taka rawar gani a kafa APC
Awujale ya assasa kafa jam'iyyar APC Hoto: @Mbuhari
Source: Twitter

Fasto Tunde Bakare ya bayyana haka ne yayin jawabinsa na “halin da ƙasa ke ciki” a ranar Lahadi a dakin taron cocin, cewar rahoton jaridar Daily Trust.

Kara karanta wannan

Duk da suna cikin hadaka, El Rufai da Peter Obi sun ki komawa ADC, an ji dalili

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar Fasto Bakare, rasuwar waɗannan mutane biyu a rana ɗaya wani iko ne na ubangiji.

Yadda Awujale ya taka rawar kafa APC

Ya tuna cewa, ko da yake Awujale ba ɗan siyasa ba ne, amma ya taka rawa sosai wajen haɗa jam’iyyun adawa waje guda, wanda hakan ya haifar da jam’iyyar APC inda har ya kai ga nasarar Buhari a zaɓen 2015.

Ya bayyana yadda ya tunkari Awujale don ya roƙi Tinubu da ya jagoranci batun haɗewar jam’iyyun, wanda ya amince da hakan.

Fasto Bakare ya ƙara da cewa, da marigayi sarkin wanda ya rasu yana da shekara 92 bai shiga tsakani wajen wannan haɗin gwiwa ba, da kuwa APC ba ta samu ba.

"Ba tare da rawar ganin da Awujale ya taka ba, da APC ba za ta samu a matsayin jam’iyya ba."
"Mai martaba (Kabiyesi) ne ya kira wani muhimmin taro a otal ɗin Oriental da ke Victoria Island, inda aka cimma matsaya wacce ta haifar da kafuwar jam’iyyar APC."

Kara karanta wannan

An fara watsewa Tinubu bayan cikawar Buhari, tsohon shugaban APC ya shiga ADC

"Duk da hakan, Kabiyesi bai tsaya ga wata jam’iyya ba, yana goyon bayan duk wani yunƙuri da yake ganin zai kawo nagartaccen mulki, ya ƙarfafa muradun ƙasa, ya bunƙasa zaman lafiya, da kuma gina Najeriya ɗaya.”
“Har zuwa lokacin rasuwarsa, ya kasance dattijo nagari, ɗan ƙasa na gari, mai ba da shawara, aboki na gaske, kuma wata baiwar Allah ga ƙasarmu."

- Fasto Tunde Bakare

Tunde Bakare ya yi magana kan kafa APC
Tunde Bakare ya yi takara tare da Buhari a 2011 Hoto: @tundebakare, @MBuhari
Source: Twitter

Fasto Bakare ya magantu kan kafa APC

Fasto Bakare ya jaddada cewa haɗakar da aka yi da ta haifar da APC shi ne karon farko da masu kishi daga Arewacin Najeriya da na Kudancin Najeriya suka haɗa hannu waje guda, wani abu da ba a taɓa samu ba a baya.

Ya ce rasuwar waɗannan mutane biyu manya na nuna wata alama ce ta samun sauyi, wanda ƴan kaɗan ne kawai za su iya fahimta.

Sanata Binani ta fice daga APC zuwa ADC

A wani labarin kuma, kun ji cewa tsoguwar ƴar takarar gwamnan jihar Adamawa, Sanata Aishatu Binani ta fice daga jam'iyyar.

Sanata Binani wacce ta taɓa wakiltar Adamawa ta Tsakiya a majalisar dattawa ta koma jam'iyyar haɗaka ta ADC.

Ta bayyana cewa za su yi tafiya a cikin ADC wacce ke ci gaba da samun manyan ƴan siyasa da suke komawa cikinta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng