'Yadda Buhari Ya Yaƙi Bankin Duniya da IMF domin Kare Talakan Najeriya'

'Yadda Buhari Ya Yaƙi Bankin Duniya da IMF domin Kare Talakan Najeriya'

  • Tsohon shugaban kungiyar kwadago, Ayuba Wabba, ya yi jimamin rasuwar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari
  • Wabba ya bayyana rasuwar Buhari a matsayin babban rashi ga talakawa da ma'aikata saboda manufofinsa na jin kai
  • Kwamred Wabba ya ce Buhari ya ki cire tallafin mai duk da matsin lamba daga IMF da Bankin Duniya saboda yan Najeriya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

FCT, Abuja - Tsohon shugaban kungiyar kwadago, NLC da ITUC, Ayuba Wabba, ya yi jimamin rasuwar Muhammadu Buhari.

Wabba ya ce rasuwar Buhari babban rashi ne ga ma’aikata da talakawan Najeriya baki daya.

An yabawa Buhari kan kare talakawa a Najeriya
An yabawa Buhari kan kin cire talalfi saboda talakawa. Hoto: Muhammadu Buhari.
Source: Twitter

Yadda ma'aikata suka amfana da Buhari

Vanguard ta ce Wabba ya bayyana rasuwar Buhari abin bakin ciki ne, musamman ga ma’aikatan da suka amfana da manufofinsa masu tausayi.

Kara karanta wannan

'Ya taɓa korarmu kan N15': Diyar Buhari game da tarbiyya da mahaifinsu ya ba su

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wabba ya tuna lokacin da dattijon ya hau mulki a 2015, Buhari ya amince da tallafin dala biliyan 2.1 don biyan albashi da fansho.

Ya ce:

“Abin da aka shirya a matsayin duban lafiya a London ya rikide zuwa rasuwar shugaban da ya tsaya tsayin daka tare da talakawa.
“Ya damu matuka da halin da ma’aikata ke ciki. Ya tambayi gwamnoni yadda suke iya barci yayin da ma’aikata ke binsu bashi."
An fadi alherin Buhari ga talakawan Najeriya
Tsohon shugaban kwadago ya yabawa mulkin Buhari. Hoto: Muhammadu Buhari.
Source: Twitter

Tallafin Buhari da wasu jihohi suka cinye

A 2017, Buhari ya sake sakin bilyoyin Naira domin taimaka wa jihohi biyan albashi da fansho.

Ayuba Wabba ya jinjinawa Buhari kan tattaunawar mafi karancin albashi da ya yi a lokacin mulkinsa.

“Abin takaici, wasu gwamnoni sun karkatar da kudin, Buhari ya gabatar da adadin da ya fi N30,000 kafin gwamnoni su hana hakan."

- Cewar Wabba

Wabba ya ce babbar manufar Buhari da ta yi amfani ga talakawa ita ce kin cire tallafin man fetur duk da matsin lamba daga Hukumar IMF da wasu a waje.

Kara karanta wannan

Ana ci gaba da bayyana ayyukan alheran Buhari, Malami faɗI abin da ya sani

Ya kara da cewa:

“Duk da matsin lamba daga IMF da Bankin Duniya, Buhari ya ki kara farashin mai domin kare rayuwar talakawa."

Ya ce tarihi ba zai auna shugabanni da jawabi ba, sai dai da tasirin da suka yi a rayuwar al’umma, musamman ma’aikata da talakawa.

Wabba ya roki Allah ya gafarta wa Buhari, ya sa ya huta ya kuma ba shi gidan aljanna firdausi madaukakiya.

“Buhari ya bambanta a inda ya fi muhimmanci, wajen taimaka wa ma’aikata, ‘yan fansho da matalauta.
"Ina mika ta’aziyya ga Aisha Buhari da danginsa baki daya"

- Ayuba Wabba

Jigon ADC ya ce babu kamar Buhari

Kun ji cewa jigo a ADC, Salihu Lukman ya yi magana kan irin ƙalubalen da jagororin haɗaka za su iya fuskanta kan zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.

Salihu Lukman ya bayyana cewa a cikin haɗaka babu mutum mai tasiri irin na tsohon shugaban ƙasa, marigayi Muhammadu Buhari.

Tsohon jigo a APC ya buƙaci ƴan haɗakar da su zama masu ƙanƙan da kai tare da gina ɗabi'ar yin aiki tare idan suna son samun nasarar kafa gwamnati a Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.