Shettima, Atiku, Gwamnoni da Jiga Jigan da Suka Koma Gidan Buhari Awanni 24 bayan Birne Shi

Shettima, Atiku, Gwamnoni da Jiga Jigan da Suka Koma Gidan Buhari Awanni 24 bayan Birne Shi

  • Mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima tare da gwamna Dikko Radda sun halarci addu'ar uku a gidan Muhammadu Buhari
  • An gudanar taron addu'ar ne domin rokon Allah gafarta wa tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ranar Laraba a Daura
  • Manyan jiga-jigan siyasa, ministoci na yanzu da tsofaffi sun halarci wannan addu'a ta bayan kwanaki uku da rasuwar Buhari

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Katsina - An gudanar da taron addu'ar uku domin rokon Allah Ya jikan tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari a gidansa na Daura a jihar Katsina.

Taron ya haɗa manyan ’yan siyasa daga ɓangarori daban-daban, ciki har da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar.

Taron addu'ar uku.
Taron addu’ar ukun Buhari ya hada Shettima, Atiku, Peter Obi da wasu jiga-jigan siyasa a Daura Hoto: @OfficialSKSM
Source: Twitter

Sanata Shettima ya tabbatar da hakan a wani saƙo mai haɗe da hotuna da ya wallafa a shafinsa na X jiya Laraba.

Kara karanta wannan

Wata sabuwa: Za a yi wa shugaba Buhari addu'a a coci ranar Lahadi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An gudanar da addu'ar uku a gidan Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Raɗɗa da takwaransa na jihar Borno, Farfesa Babagana Umaru Zulum sun halarci taron addu'ar a Daura.

Bayan kammala addu’o'i, Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana cewa rasuwar Buhari ta girgiza Shugaba Bola Ahmed Tinubu matuƙa.

Ya ce mutuwar Buhari babban rashi ne ba wai ga iyalinsa ko mutanen Daura ko na Jihar Katsina kaɗai ba, har ma da ƙasa baki ɗaya da nahiyar Afirka.

Shettima ya ƙara da cewa mutane daga sassa daban-daban na duniya sun kira domin jajanta wa Shugaba Tinubu bisa wannan babban rashi.

Ya yi addu’a ga Allah da ya jikansa da rahama, ya gafarta masa, ya sanya shi cikin Aljannatul Firdaus, tare da kare iyalansa da ya bari, kamar yadda Daily Trust ta kawo.

Jerin waɗanda suka koma gidan Buhari

Daga cikin manyan baki da suka halarci taron addu'ar akwai:

Kara karanta wannan

Atiku da El Rufa'i sun ziyarci kabarin Buhari kwana 1 da birne shi

1. Gwamnan Katsina, Malam Dikko Radda

2. Gwamnan Borno, Fafesa Babagana Umaru Zulum

3. Ministar Harkokin Mata, Imaan Suleiman-Ibrahim

4. Ministan Noma da Samar da Abinci, Sanata Abubakar Kyari

5. Ministan Muhalli, Alhaji Balarabe Abbas

6. Ministan Kasafin Kuɗi da Tsare-tsare, Sanata Abubakar Bagudu

7. Ministan Shari’a kuma Antoni-Janar na Tarayya, Lateef Fagbemi (SAN)

8. Ƙaramar Ministar Babban Birnin Tarayya (FCT), Dr. Mariya Mahmoud

9. Ministan Ma’adanai da Bunkasa Karafa, Prince Shaibu Abubakar

10. Ƙaramin Ministan Ayyuka, Barr. Bello Goronyo

11. Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a 2023

12. Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Ambasada Babagana Kingibe

13. Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar

14. Tsohon Daraktan Hukumar Leken Asiri ta Ƙasa (NIA), Rufai Ahmed

15. Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika

16. Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai

17. Tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Aminu Bello Masari

18. Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Farfesa Isah Ali Pantami

Kara karanta wannan

Yadda Atiku ya baro kasar waje, ya iso cikin dare domin jana'iza da makokin Buhari

19. Tsohon Ministan Abuja, Malam Musa Bello

20. Sarkin Daura, Mai Martaba Alhaji Umar Farouk

21. Tsohon Ministan Ruwa, Malam Suleiman Adamu da sauransu.

Buhari: Ministan Tinubu ya soki Atiku

A wani labarin, kun ji cewa Festus Keyamo (SAN) ya nuna takaicinsa kan yadda Atiku ya saki takardar barin PDP ana tsakiyar jimamin rasuwar Muhammadu Buhari.

Ministan sufurin jiragen sama ya ce bai kamata tsohon mataimakin shugaban ƙasa, ya fitar da wasikar ficewarsa daga PDP a daidai lokacin da Najeriya ke alhini ba.

Keyamo ya kalubalanci Atiku kan amfani da Tambarin Gwamnatin Tarayya, a cikin wasiƙarsa, yana mai cewa hakan ya sabawa doka.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262