Jerin Sunayen Sabbabin Jihohi 37 da Aka Buƙaci Ƙirƙirowa a Kano da Sauran Sassan Najeriya

Jerin Sunayen Sabbabin Jihohi 37 da Aka Buƙaci Ƙirƙirowa a Kano da Sauran Sassan Najeriya

  • Majalisar Wakilai ta karɓi buƙatu 46 na kirƙiro sababbin jihohi a faɗin Najeriya yayin da take shirye-shiryen yi wa kundin tsarin mulki garambawul
  • Majalisar ta karɓi waɗannan buƙatu ne ta hannun kwamitin da ta ɗora wa alhakin aikin gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999
  • Daga cikin wadannan buƙatu da aka miƙa wa kwamitin, an nemi ƙirƙiro sababbin jihohi 37 a faɗin yankunan Najeriya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Kwamitin Majalisar Wakilai ta Tarayya ya bayyana cewa zuwa yanzu, ya karɓi buƙatu 46 da suka nemi ƙirƙiro sababbin jihohi a faɗin Najeriya.

Kwamitin majalisar wanda aka ɗorawa alhakin gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999, ya ce an kuma shigar da wasu buƙatu 117 na ƙirƙiro ƙarin ƙananan hukumomi.

Majalisar Wakilan Tarayya.
An shigar da buƙatu 46 na kirkiro sababbin jihohi a Majalisar Tarayya Hoto: @HouseNGR
Source: Facebook

Tribune Najeriya ta tattaro cewa wadannan ƙudurori da aka shigar daga kungiyoyi da dama sun shafi dukkanin shiyyoyin siyasa guda shida na ƙasar nan.

Kara karanta wannan

2027: Shugaban ADC ya fallasa shirin dakile farin jinin jam'iyyar

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jerin sunayen sababbin jihohi 37 da aka buƙata

Legit Hausa ta haɗa maku cikakken jerin sunayen jihohin da ake neman ƙirƙirowa kamar yadda kwamitin ya fitar:

Arewa maso Gabas

1. Jihar Savannah — daga Jihar Borno

2. Jihar Kwararafa — daga Jihar Taraba

3. Jihar Katagum— daga Jihar Bauchi

4. Jihar Amana — daga Jihar Adamawa

5. Jihar Sardauna — daga Jihar Taraba

6. Jihar Muri — daga Jihar Taraba

Arewa maso Yamma

7. Jihar Gurara — daga Jihar Kaduna

8. Sabuwar jihar Kaduna — daga Jihar Kaduna

9. Jihar Hadejia — daga Jihar Jigawa

10. Jihar Gobir — daga Jihar Sokoto

11. Jihar Kainji — daga jihohin Kebbi da Neja

12. Jihar Tiga — daga Jihar Kano

13. Jihar Ghari — daga Jihar Kano

Arewa ta Tsakiya

14. Edu State — daga Jihar Neja

15. Jihar Okun — daga Jihar Kogi

16. Jihar Okura — daga Jihar Kogi

Kara karanta wannan

'Yadda Buhari ya ki karbar sababbin motocin N400m a Villa', Garba Shehu

17. Jihar Kudancin Filato — daga Jihar Filato

18. Jihar Lowland — daga Jihar Filato

19. Jihar Filato Sabon Yanki — daga Jihar Filato

20. Sabuwar jihar Kogi — daga jihohin Kogi, Nasarawa da Edo

21. Jihar Ifesowapo — daga Jihar Kwara

22. Jihar Abuja — daga babban birnin tarayya (FCT)

23. Jihar Apa — daga Jihar Benuwai

24. Jihar Apa-Agba — daga Jihar Benuwai

25. Jihar Ayatutu — daga Jihar Benuwai

Kudu maso Gabas

26. Jihar Orashi — daga Anambra, Imo da Ribas

27. Jihar Orlu — daga yankin Kudu Maso Gabas

28. Jihar Anioma — daga yankin Kudu Maso Gabas

29. Jihar Etiti — daga yankin Kudu Maso Gabas

30. Jihar Aba — daga yankin Kudu Maso Gabas

31. Jihar Adada — daga Jihar Enugu

Kudu maso Kudu

32. Jihar Atlantic City — daga Jihar Ribas

33. Jihar Bori — daga Jihar Ribas

34. Jihar Iwuroha — daga Jihar Ribas

35. Jihar Obolo — daga Jihar Akwa Ibom

Kara karanta wannan

An buƙaci a raba Kano zuwa jihohi 2 da ƙirƙiro sababbin ƙananan hukumomi 26

36. Jihar Warri — daga Jihar Delta

37. Jihar Toru-Ebe — (babu cikakken bayani, yana yiwuwa daga Bayelsa)

An buƙaci raba Kano zuwa jihohi 2

A wani rahoton, kun ji cewa Kano ta buƙaci a raba ta zuwa jihohi biyu tare da kirkiro ƙarin ƙananan hukumomi 26 daga cikin 44 da ake da su a yanzu.

Hakan na cikin shawarwarin da gwamnatin Kano ta miƙa wa kwamitin gyaran kundin tsarin mulki a tarom jin ra'ayoyin jama'a da aka yi a Kaduna.

Ta ce hakan zai ƙara kusantar da gwamnati ga al'umma domin sauƙaƙa ci gaba da warware matsalolin da jama'a ke fuskanta.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262