Allahu Akbar: Gawar Tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari Ta Iso Gida Najeriya

Allahu Akbar: Gawar Tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari Ta Iso Gida Najeriya

  • A ƙarshe, gawar marigayi tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari ta iso Najeriya daga birnin Landan na ƙasar Burtaniya
  • Tawagar gwamnatin Najeriya ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima ce ta yiwa gawar rakiya tare da iyalan mamacin
  • Ana sa ran bayan kammala duk wasu tsare-tsare, Mai girma shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinibu zai karɓi gawar sannan a wuce zuwa Daura a yi mata sutura

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Katsina - Gawar marigayi tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari ta iso jihar Katsina da ke Arewa maso Yammacin Najeriya.

Tawagar gwamnatin Najeriya ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima ce ta yiwa gawar rakiya daga Landan zuwa Katsina.

Jirgin da ya ɗauko gawar Buhari ya isa Katsina.
Gawar Muhammadu Buhari ta isa jihar Katsina Hoto: Nigeria Air Force
Source: Twitter

Jaridar TVC News ta tabbatar da wannan labari a wani gajeren saƙo da ta wallafa a shafinta na X da tsakar rana yau Talata.

Kara karanta wannan

Duniya kenan: Yadda aka binne gawar Muhammadu Buhari a Daura

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kashim Shettima ya iso tare da gawar Buhari

Sanata Shettima da iyalan tsohon shugaban ƙasa ne suka yiwa gawar Buhari rakiya tun daga Landan zuwa Katsina.

A bidiyon da Imran Muhammad ya wallafa a shafin X, an ga lokacin da jirgin rundunar sojin saman Najeriya, wanda ya ɗauko gawar Buhari ya sauka a filin jirgin Umaru Musa Yar'adua da ke birnin Katsina.

Ana sa ran shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, mataimakinsa, Kashim Shettima, gwamnoni, ministoci da manyan jami'an gwamnati da al'umma za su yi wa gawar rakiya zuwa Daura.

Tawagar gwamnatin Najeriya da ta ɗauko Buhari

Tun farko dai Sanata Kashim Shettima ya tafi birnin Landan ne bisa umarnin shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu domim cika duka wasu shaɗuɗɗa da ɗauko gawar Buhari zuwa gida.

Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a ranar Lahadi a birnin London, za a birne shi yau Talata, 15 ga watan Yuli, 2025 a gidansa da ke Daura, Jihar Katsina.

Kara karanta wannan

An tafi da gawar Buhari zuwa mahaifarsa Daura bayan ta iso Najeriya

Tawagar Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima ta haɗa da Shugaban Ma’aikatam fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila da Gwamnan Jihar Borno Farfesa Babagana Zulum.

Marigayi shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.
Tawagar gwamnatin tarayya da ta ɗauko hawar Buhari ta isa Katsina Hoto: Muhammadu Buhari
Source: Twitter

Sauran sun haɗa da Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Tuggar, da Mataimakin Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa Sanata Ibrahim Hassan Hadejia.

Wannan tawaga da Tinubu ya tura Landan sun yi duk abin da ya kamata har aka ɗauko gawar Buhaɗi zuwa gida Katsina cikin mutunci, ƙima da girmamawa.

Tawagar Shettima na tare da iyalan Bubari, wanda suka haɗa da mai ɗakinsa. Hajiya Aisha Muhammadu Buhari da wasu daga cikin ƴaƴan marigayin.

Adesina ya kare Buhari kan zuwa neman lafiya

A wani rahoton, kun ji cewa Femi Adesina, ya ce da Muhammadu Buhari ya dogara da asibitocin Najeriya wajen kula da lafiyarsa, watakila da tuni ya rasu.

Ya bayyana cewa likitocin da ke kula da lafiyar Buhari tun kafin 2015 sun san tarihin lafiyarsa sosai, don haka ba hikima ba ce a sauya su a tsakiyar jinya.

Tsohon kakakin shugaban ƙasar ya ce dole sai yana raye ne zai yi ƙoƙarin gyara harkar lafiyar ƙasar nan, yana mai cewa dama tun kafin ya hau mulki yana zuwa Landan.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262