Gwamna Radda Ya Sanar da Wurin da Za a Yi Jana'izar Shugaba Muhammadu Buhari

Gwamna Radda Ya Sanar da Wurin da Za a Yi Jana'izar Shugaba Muhammadu Buhari

  • Gwamnan jihar Katsina, Malam.Dikko Umaru Raɗɗa ya tabbatar da rasuwar tsohon shigaban ƙasa, Muhammasu Buhari a Landan
  • Dikko Raɗɗa ya bayyana cewa za a yi jana'izar Buhari yau Litinin, 14 ga watan Yuli, 2025 a gidansa da ke Daura a jihar Katsina
  • Gwamna Radda ya kuma miƙa sakon ta'aziyya ga al'ummar Katsina da Najeriya bisa wannan rashi na uba da aka yi

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Katsina - Da yammacin jiya Lahadi, 13 ga watan Yuli, 2025 aka samu labarin rasuwar tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari.

Iyalan marigayin sun sanar da cewa Buhari ya rasu ne a wani asibiti a birnin Landan na ƙasar Ingila bayan fama da rashin lafiya.

Gwamnan Katsina ya tabbatar da rasuwar Buhari.
Malam.Dikko Radda ya ce za a yi jana'izar Buhari a Daura Hoto: Ibrahima Kaulaha Mohammed
Source: Facebook

Sai dai a wata hira da DW Hausa ta yi da shi, gwamnan Katsina, Malam Dikko Raɗɗa ya ce za a yi jana'izar Buhari a gidansa da ke Daura.

Kara karanta wannan

Gwamnonin Arewa 7 su haɗa baki, sun ba da hutun kwana 1 saboda rasuwar Buhari

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Raɗɗa ya ce yana ƙasar Ingila lokacin da Allah ya karɓi rayuwar Buhari, domin ya je duba shi tun ranar Juma'a da ta gabata.

Gwamnan Katsina ya tabbatar da rasuwar Buhari

Da yake tabbatar da rasuwar Buhari, Malam Dikko Raɗɗa ya ce:

"InnalilLahi wa inna ilaiHi ra'i'un, Allah Shi yake da rayuwa kuma Ya karɓi ran babanmu, ubanmu, uban ƙasar nan, Muhammadu Buhari.
"Kuma muna yi wa mutanen Katsina da ɗaukacin ƴan Najeriya ta'aziyyar wannan rashi saboda wannan rashi ba namu ba ne kaɗai, na ƙasarmu ne.
"Mun rasa jagora wanda rayuwarsa gaba ɗaya ya kafa ta a kan yadda zai taimaki talaka da yadda talaka zai samu sauƙi na rayuwa. Ba a taɓa yin ɗan siyasar da ya samu martaba da ƙauna kamar yadda ya samu ba a rayuwarsa."

Dikko Raɗɗa ya bayyana cewa yana shirin dawowa gida bayan ya je duba lafiyar Buhari, kwatsam kuma Allah ya ƙarɓi rayuwarsa.

Kara karanta wannan

Shin ya kamata ƴan Najeriya su yafewa Buhari? Sheikh Aminu Daurawa ya roƙi abubuwa 2

Tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari.
Gwamnan Katsina ya bayyana shirin da aka yi na jana'izar tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari Hoto: @MBuhari
Source: Twitter

A ina za a yi jana'azar Buhari?

Da aka tambaye shi kan ina za a yi jana'iza, gwamnan ya ce ya yi magana da iyalan mamacin kuma sun cimma matsayar cewa za a yi masa sutura a mahaifarsa watau Daura.

"Yanzu muka rabu da iyalansa a asibitin da ya rasu, kuma an yi ittifaƙin za a kai shi gida Najeriya a Katsina, a Daura domin a yi ma shi sutura.
"Kuma in Sha Allahu da safe za su baro Ingila domin mataimakin shugaban ƙasa ya taso daga Najeriya zai zo ya tafi da gawar bisa umarnin shugaban ƙasa."
"Za mu koma Katsina mu tare su daga nan mu wuce Daura inda za a masa sutura da izinin Allah.

- Gwamna Dikko Raɗɗa.

Gwamnan ya ƙara da cewa idan komai ya tafi yadda aka tsara, za a yi jana'izar Buhari a Daura da La'asar yau Litinin, 14 ga watan Yuli, 2025.

Kara karanta wannan

Tuna baya: Yadda Buhari ya tsira bayan yunkurin kashe shi a 2014

Abubuwan da za a tuna Buhari da su

A wani labarin, mun kawo maku wasu abubuwan da suka faru a mulkin marigayi Muhammadu Buhari da ba za a manta da su ba.

Muhammadu Buhari ya shafe wani lokaci yana jinya a birnin London bayan ya sauka a mulki shekaru biyu da suka wuce, kafin Allah ya karɓi ransa.

Rasuwar Shugaba Buhari ta girgiza Najeriya baki daya wanda al'umma suke yi masa fatan samun gafara da rahamar Allah.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262