Majalisa Ta Kira Gwamna, Tsofaffin Gwamnoni, Jami'an Tsaro kan Kashe Kashe

Majalisa Ta Kira Gwamna, Tsofaffin Gwamnoni, Jami'an Tsaro kan Kashe Kashe

  • Kwamitin wucin gadi kan rashin tsaro a Filato ya fara laluben yadda za a magance asarar rayuka a sassa daban-daban na jihar
  • Kwamitin ya gayyaci Gwamna Caleb Mutfwang, tsofaffin gwamnoni da shugabanni domin neman mafita kan rikice-rikicen
  • Taron zai hada da shugabannin addini, hukumomin tsaro, kungiyoyin matasa da na farar hula, da kungiyoyin wanzar da zaman lafiya

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT Abuja – Kwamitin wucin gadi na Majalisar Wakilai kan matsalolin tsaro a jihar Filato ya bayyana damuwa matuka kan tabarbarewar tsaro a jihar.

Wannan ta sa ya gayyaci Gwamna Caleb Mutfwang, tsofaffin gwamnonin jihar da sauran shugabannin al’umma domin halartar babban taron tsaro na musamman.

Ana fama da rikici a Filato
Majalisa za ta zauna da gwamnan Filato Hoto: Caleb Muftwang/House of Representatives, Federal Republic of Nigeria
Source: Facebook

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa taron zai mayar da hankali ne kan shawo kan tashe-tashen hankula da kashe-kashen da ke faruwa a jihar Filato.

Kara karanta wannan

UAE ta ƙaƙaba takunkumi game da shiga kasarta ga wasu rukunin 'yan Najeriya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majalisa na nemawa Filato mafita

BBC Hausa ta wallafa cewa shugaban kwamitin, Dr. Wale Hammed, ya ce taron wani bangare ne na kokarin tattara shawarwari da hanyoyin magance matsalar rikici a Filato..

Ya kara da cewa ana yawan kashe mutane a yankunan Bokkos, Bassa da Mangu—inda kisan gilla da hare-hare suka zama ruwan dare ga yan gari da matafiya.

Dr. Hammed ya kuma bayyana cewa an buɗe kafa domin karɓar ra’ayoyi da shawarwarin jama’a daga masu ruwa da tsaki, domin tabbatar da warware matsalolin.

Ya ce:

“Majalisa ita ce za ta iya fuskantar kalubalen kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa. Wannan taro na neman mafita ne, ba don kara rarrabuwar kawuna ba.”

Ana fama da kashe-kashe a Filato

Majalisa ta ce an shirya taron bayan muhawara a majalisa a watan Mayu da Yuni kan kashe mutane 13 a Rimi, Basawa Sabon, a Mangu da kuma sauran hare-hare.

Kara karanta wannan

Najeriya ta yi rashi, tsohon shugaban majalisar wakilai ya rasu

Dr. Hammed ya ce kwamitin yana aiki ne bisa tanadin sashe na 88 da 89 na Kundin Tsarin Mulki na 1999, domin tabbatar da adalci da samun sahihiyar fahimta daga masu ruwa da tsaki.

Daga cikin wadanda ake sa ran za su halarci taron akwai: Gwamna Caleb Mutfwang, da tsofaffin gwamnonin Filato: Simon Lalong, Jonah Jang da Joshua Dariye

Majalisar wakilan Najeriya
Majalisa za ta gudanar da taro kan rashin tsaro Hoto: House of Representatives
Source: Facebook

Sai kuma Sanatoci da ‘yan majalisar wakilai daga jihar, da shugabannin kananan hukumomi da sarakunan gargajiya da shugabannin addinai, kungiyoyin matasa da farar hula.

Sauran su ne shugabannin hukumomin tsaro: Sojoji, ‘Yan sanda, DSS, NSCDC da jami’an 'Operation Safe Haven' na yanzu da na baya da kungiyoyin CAN, JNI da Miyetti Allah.

Yan bindiga sun tare jama'a a Filato

A baya, kun samu labarin cewa wasu ‘yan bindiga sun kai mummunan hari kan wasu mutane a kauyen Rim da ke karamar hukumar Riyom, jihar Filato.

Maharan sun farmaki wasu matasa da ke dawowa daga jana’iza, suka harbi mutum daya sannan suka yanke hannunsa, yayin da suka jefa jama'a a firgici.

Masu makokin dai sun fito ne daga jana’izar wani mamaci a kauyen Bachit, kafin ‘yan bindigar su tare su a hanya suna dawowa gida tare da yi masu ɓarna.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng