NAHCON Ta Samu Tsaiko a Jigilar Alhazan Najeriya zuwa Gida, Za Su Ƙara Zama a Saudiyya

NAHCON Ta Samu Tsaiko a Jigilar Alhazan Najeriya zuwa Gida, Za Su Ƙara Zama a Saudiyya

  • Hukumar Hajji ta Ƙasa watau NAHCON ta ɗage ranar kammala jigilar mahajjatan Najeriya daga ƙasar Saudiyya zuwa gida
  • NAHCON ta ce an samu tsaiko ne sakamakon cunkoson jiragen da ake samu a filayen Saudiyya saboda kowace ƙasa na ƙoƙarin kwashe alhazanta
  • A halin yanzu, ana sa ran kammala kwaso alhazan Najeriya zuwa gida a ranar 2 ga watan Yuli, maimakon 28 ga watan Yuni da aka tsara tun farko

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta sanar da ƙarin wa’adin kammala jigilar Mahajjatan Najeriya na 2025 zuwa gida daga ƙasar Saudiyya.

Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da mataimakiyar darakta kuma mai magana da yawun hukumar NAHCON ta ƙasa, Fatima Usara, ta fitar a ranar Alhamis.

Mahajjata da shirin dawowa gida.
NAHCON ta tsaiwata lokacin jigilar alhazan Najeriya zuwa gida Hoto: @NigeriaHajjCom
Source: Twitter

Hukumar ta ce ba za a iya kammala jigilar mahajjatan zuwa gida a ranar 28 ga Yuni kamar yadda aka tsara tun da farko ba, Premium Times ta rahoto.

Kara karanta wannan

Kotu ta yi hukunci kan bukatar Firaministan Isra'ila bayan kammala yaƙi da ƙasar Iran

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

NAHCON ta ɗaga ranar gama kwaso mahajjata

"Lokaci ya ƙure, aikin dawo da mahajjata gida sai ya kai har zuwa ranar Talata, 2 ga Yuli, 2025, idan babu wani cikas da ya taso daga baya,” in ji ta.

Fatima Usara ta kuma bayyana yawan mahajjatan da suka rage, da adadin sawun da kamfanoni jiragen sama za su yi kafin kamma dawo da ƴan Najeriya gida.

Adadin mahajjatan Najeriya da suka rage a Saudiyya

"Kamfanin Max Air na da ragowar mahajjata 6,019 da zai kwaso zuwa gida, kuma yana amfani da jirage biyu masu kujeru 560, wato jimillar kujeru 1,120 a rana.
"Sai kuma UMZA Aviation Services, yana da ragowar mahajjata 4,850, shi ma dai jirage biyu gare shi waɗanda ke iya ɗauko mutum 796 a rana.
"FlyNas, yana da mahajjata 2,480 da zai dawo da su gida, kamfanin na da ƙarfin ɗauko fasinjoji 819 a kullum. Na karshe, Air Peace, wanda ke daga ragowar mahajjata 1,635 da zai kwaso zuwa Najeriya."

Kara karanta wannan

ADA: INEC ta yi bayani kan yiwa jam'iyyu rajista gabanin 2027

- Fatima Usara.

Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan.
NAHCON ta ce za a gama dawo da ƴan Najeriya da suka sauke farali a bana zuwa gida a watan Yuli Hoto: Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan
Source: Twitter

Meyasa aka samu jinkirin kwaso alhazan Najeriya?

NAHCON ta roƙi mahajjatan Najeriya da har yanzu suke a Saudiyya da su yi haƙuri da jinkirin da aka sanu wajen dawo da su gida.

Hukumar ta bayyana cewa cunkosom jiragen sama daga ƙasashen duniya ne ya haddasa wannan jinkirin, rahoton The Cable.

“Don Allah a lura cewa ƙarancin jigilar jirage da ake gani a yanzu wajen dawo da mahajjata gida yana da nasaba da cunkoson zirga-zirgar jirage da ke faruwa a ƙasar Saudiyya bayan gama aikin Hajj."
“A wannan lokaci ne ƙasashe da dama ke ƙoƙarin kwashe 'yan ƙasarsu zuwa gida, kuma hakan na haifar da cunkoso a filayen jiragen saman Saudiyya," im ji Fatima.

Jihohi 11 sun tallafawa alhazai a Saudiyya

A wani labarin, kun ji cewa mahajjatan Najeriya daga jihohi 11 sun samu tallafi daga gwamnoninsu yayin da suke gudanar da aikin Hajjin bana a Saudiyya.

Ana lissafin cewa jihohin guda 11 sun ba da tallafin N6.2bn domin sauƙaƙawa Alhazan yayin da suke zaune a ƙasa mai tsarki.

Wannan dai na ɗaya daga cikin taimakon da gwamnonin jihohi suka yi wa mahajjatansu, domin tabbatar da walwala da jin daɗinsu.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262