Tinubu Ya Kunyata Majalisar Tarayya, Ya Ƙi Sanya Hannu a Ƙudurin Dokar NDLEA

Tinubu Ya Kunyata Majalisar Tarayya, Ya Ƙi Sanya Hannu a Ƙudurin Dokar NDLEA

  • Shugaba Bola Tinubu ya ƙi sanya hannu kan ƙudirin dokar NDLEA saboda ya saɓa wa wasu dokokin rarraba kuɗi na gwamnati
  • Wannan shi ne karo na biyu a wannan makon da Tinubu ya ƙi amincewa da sanya hannu kan kudiri, saboda rashin daidaitonsu da doka
  • Duk da haka, ana sa ran Tinubu zai sanya hannu kan sababbin kudirorin gyaran haraji huɗu da za su kawo sauyi a tattalin arzikin Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Shugaba Bola Tinubu ya ƙi sanya hannu a kan sabon kudirin dokar hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA Bill, 2025).

An bayyana matsayar shugaban ƙasar ne a cikin wata wasiƙa da kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, ya karanta a zaman majalisar na ranar Alhamis.

Shugaba Bola Tinubu ya ki amincewa da kudurin dokar NDLEA da aka gabatar masa
Shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu. Hoto: @officialABA
Source: Twitter

Bola Tinubu ya ki amince wa da kudurin NDLEA

Kara karanta wannan

Ta faru ta kare: Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin gyaran haraji 4

Kudirin dokar yana neman bai wa NDLEA ikon riƙe wani kaso na kuɗaɗen da aka samu daga laifuffukan da suka shafi miyagun ƙwayoyi, inji rahoton Channels TV.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Amma Shugaba Tinubu ya ce wannan mataki ya saɓa wa dokokin kuɗi da ake amfani da su a halin yanzu.

A cikin wasiƙar Tinubu, ya bayyana cewa a ƙarƙashin tsarin da ake bi yanzu, "Ana saka duk kuɗaɗen da aka samu daga aikata laifuffuka a cikin asusun gwamnati na mallakar kadarorin da aka kwace."

Ya ƙara da cewa:

"Za a iya raba kuɗaɗe ga kowace hukumar da ke da alhakin kwato kadarori, ciki har da NDLEA, ne kawai ta hanyar amincewar shugaban ƙasa, bayan samun izinin majalisar zartarwa ta tarayya da majalisar dokoki ta kasa."

Tinubu ya ce tsarin da ake bi a halin yanzu yana tabbatar da riƙon amana da kuma sa ido kan kudaden da aka kwato, don haka babu buƙatar canza shi.

Sau 2 Tinubu na kin amincewa da kudirori

Kin amincewa da kudirin NLEA a ranar Alhamis shine karo na biyu a wannan makon da Shugaba Tinubu ya ƙi sanya hannu a kan wani kudiri.

Kara karanta wannan

Mataimaki a 2027: Barau ya fadi shirinsa kan yin aiki da Shugaba Tinubu

Tun a ranar Talata, ya ƙi amincewa da kudirin dokar gidauniyar dakin karatu ta majalisar dokoki ta kasa ta 2025.

Shugaba Tinubu ya ce ya ki sanya hannu kan kudurorin ne saboda rashin daidaito da manufofin dokokin tarayya, musamman game da samar da kuɗi ga hukumomi, haraji, da tsarin albashi.

Ana sa ran Shugaba Bola Tinubu zai sanya hannu kan kudurorin gyaran haraji a yau
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu yayin da yake jawabi ga majalisar tarayya. Hoto: @officialABAT
Source: Twitter

Tinubu zai sa hannu kan dokokin haraji 4

Duk da haka, ana sa ran zai sanya hannu kan sababbin kudirorin gyara haraji guda huɗu, waɗanda za su kawo sauyi a tsarin kuɗi da tattalin arziki na Najeriya.

Kudirorin guda huɗu su ne: Kudirin haraji na Najeriya, kudirin dudanar da haraji na Najeriya, kudirin kafa hukumar haraji ta Najeriya, da kudirin kafa hukumar haɗin gwiwar haraji.

Majalisar tarayya ta amince da kudurorin gyaran harajin ne bayan shawarwari masu zurfi da aka yi da ƙungiyoyi da masu ruwa da tsaki daban-daban.

Wani dan majalisa daga Enugu ya koma APC

A wani labarin, mun ruwaito cewa, wani ɗan majalisar wakilai, Chimaobi Atu, daga jihar Enugu, ya koma jam'iyyar APC mai mulki daga jam'iyyar LP a ranar Alhamis.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya yi magana kai tsaye kan Atiku da El Rufai masu shirin kifar da shi a 2027

Hon. Chimaobi Atu ya bayyana rikicin shugabanci a cikin LP a matsayin dalilin da ya sa ya bar jam'iyyar zuwa APC.

Sauya sheƙarsa ya zo kwanaki biyu bayan Peter Akpanke, daga Cross River, Paul Nnamchi daga jihar Enugu, suka sauya sheka daga Jam'iyyar Labour zuwa APC.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com