1447 AH: Gwamna Kirista Ya ba da Hutun Sabuwar Shekarar Musulunci a Jiharsa

1447 AH: Gwamna Kirista Ya ba da Hutun Sabuwar Shekarar Musulunci a Jiharsa

  • Gwamna Seyi Makinde ya ayyana Juma’a, 27 ga Yunin shekarar 2025, a matsayin hutun ma'aikata a fadin jihar Oyo da ke Kudancin Najeriya
  • Gwamnan ya ba da hutun ne don bikin shiga sabuwar shekarar Musulunci ta 1447 AH da ake sa rai a ranar Juma'a mai zuwa
  • Sanarwar ta fito daga sakataren gwamnatin jihar, Farfesa Olanike Adeyemo, inda aka ce hutun ya shafi ma’aikatu da cibiyoyi na gwamnati baki ɗaya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ibadan, Oyo - Gwamnan Jihar Oyo, Injiniya Seyi Makinde ya zama na farko da ya fara ba da hutun sabuwar shekarar Musulunci a wannan karo.

Makinde ya ayyana Juma’a, 27 ga Yuni, 2025, a matsayin hutu domin tunawa da sabuwar shekarar Musulunci ta 1447 AH.

Gwamna ya ba da hutun sabuwar shekara
Gwamna Makinde ya ba da hutun sabuwar shekarar Musulunci. Hoto: Seyi Makinde.
Source: Facebook

Sanarwar hakan ta fito ne a cikin wata takarda da sakataren gwamnatin jiha, Farfesa Olanike Adeyemo, ya fitar a ranar Laraba, cewar Leadership.

Kara karanta wannan

'Har gida muka cin masa': Gwamnatin Zamfara ta faɗi illar da ta yi wa Bello Turji

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda Makinde ke kokarin adalci ga Musulmi

Gwamna Makinde yana kokari wurin tabbatar da cewa ya ba da hutun sabuwar shekarar Musulunci a kowace shekara da ta zagayo.

Ko a bara ma, Makinde yana kusan na farko cikin gwamnoni da suka ayyana ranar 1.ga watan Muharram a matsayin ranar hutu saboda ma'aikata su sarara.

Daga bisani, Gwamnan Oyo ya biyo bayansa duk da cewa duka gwamnonin Kiristoci ne amma an yaba musu kan kokarin yin adalci tsakanin addinai da ke jiharsu.

Gwamna ya ba al'umma shawara kan sabuwar shekara
Gwamna Seyi Makinde ya ayyana ranar Juma'a a matsayin ranar hutu. Hoto: Seyi Makinde.
Source: Facebook

Musabbabin ba da hutun sabuwar shekarar Musulunci

Gwamnan ya ce an ware wannan rana ne domin bai wa Musulmi da sauran mazauna jihar damar murnar shiga sabuwar shekarar Musulunci tare da nazarin mahimmancinta.

Gwamna Makinde ya kuma bukaci jama’a su yi amfani da damar wajen yin addu’o’i domin ci gaba da samun zaman lafiya, haɗin kai da bunƙasar Oyo da Najeriya.

Sanarwar ta ce:

“Gwamnan ya bukaci kowa da kowa da su yi amfani da wannan lokaci wajen yin addu’a domin zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban jiha da ƙasa baki ɗaya."

Kara karanta wannan

Sabuwar shekarar musulunci: Gwamnatin jihar Ƙwara ta ayyana ranar hutu

Wurare da ma'aikatu da hutun ya shafa a Oyo

Gwamnatin jihar ta ce hutun ya shafi dukkan ofisoshi da cibiyoyin gwamnati a faɗin Jihar Oyo a Kudu maso Yammacin Najeriya.

Daga bisani, gwamnan ya kuma taya al'ummar Musulmi murnar zagayowar sabuwar shekara inda ya bukaci su yi addu'o'i ga jihar Oyo da kuma siyasar da ke tunkarowa.

Gwamnonin da suka ba da hutu a bara

A baya, kun ji cewa gwamnonin jihohi a Najeriya daga Arewacin Najeriya zuwa Kudancin kasar sun ba da hutun sabuwar shekarar Muslunci ta 1446 AH.

Akalla jihohi 10 a Najeriya sun ayyana ranar Litinin 8 ga watan Yulin 2024 a matsayin ranar hutu domin murnar shigowar sabuwar shekarar Musulunci ta 1446 bayan Hijrah.

A wannan shekara ma ana sa ran jihohi da dama za su ba da hutun da ake tsammanin zai fado ranar Juma'a 27 ga watan Yunin 2025 da muke ciki.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.