Dattawan Zamfara Sun Taso Gwamna Dauda a Gaba ana Batun Dokar Ta Baci

Dattawan Zamfara Sun Taso Gwamna Dauda a Gaba ana Batun Dokar Ta Baci

  • Ƙungiyar dattawan Zamfara ta nuna damuwa kan yadda ake muzgunawa wasu zaɓaɓɓun ƴan majalisar dokokin jihar
  • A cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, ta zargi Dauda Lawal da yin amfani da ɓangaren shari'a domin ƙuntatawa ƴan majalisar
  • Ƙungiyar ta buƙaci gwamnan da ya bi hanyar neman sulhu domin warware rikicin da ke tsakaninsa da ƴan majalisar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Zamfara - Ƙungiyar dattawan Zamfara ta nuna yatsa ga Gwamna Dauda Lawal na jihar.

Ƙungigar ta zargi Gwamna Dauda Lawal da shirya wani ƙullin siyasa da ake yi wa ƴan majalisar dokokin jihar guda tara ta hanyar amfani da kotu domin danne musu haƙƙinsu.

Gwamna Dauda Lawal
Dattawan Zamfara sun caccaki Gwamna Dauda Lawal Hoto: Dauda Lawal
Source: Twitter

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin ƙungiyar, Dr. Abdulmumin Kamil Gusau, ya fitar a ranar Lahadi, 4 ga watan Mayun 2025.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Kano za ta sayowa Sanusi II motoci da kudin kananan hukumomi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dattawan Zamfara sun jefi gwamna da zargi

Dr. Abdulmumin Kamil Gusau ya bayyana matakin da gwamnatin jihar ta ɗauka a matsayin abin damuwa kuma abin kunya.

Ƙungiyar ta zargi babbar alƙalin kotun majistare, Halima Jaafar Mikaila, da bayar da sammacin kama ƴan majalisar ba tare da ba su takarda ko gabatar da tuhuma a hukumance ba, wanda hakan ya saɓawa doka.

“Muna cikin damuwa kan yadda gwamnatin jihar ke amfani da kotu wajen cin zarafin ƴan majalisar da aka zaɓa bisa doka."
"Waɗannan ƴan majalisa ana muzanta su ne saboda suna yin ayyukansu bisa tsarin doka tare da fito da kura-kurai kan yadda ake tafiyar da mulki domin amfanin jama’a."

- Dr. Abdulmumin Kamil Gusau

Ƙungiyar ta bayyana cewa ƴan majalisar da abin ya shafa waɗanda suka fito daga jam’iyyar PDP mai mulki da kuma APC da ke adawa, sun riga sun shigar da ƙara a kotun ɗaukaka ƙara da ke Sokoto.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun gwabza fada da 'yan sa kai, an samu asarar rayuka

Haka kuma sun kai ƙorafi ga hukumomi da dama, ciki har da Sufeto Janar na ƴan sanda, Darakta Janar na hukumar DSS, mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro da majalisar tarayya, domin neman shiga cikin lamarin.

Duk da waɗannan matakai da suka dauka, kungiyar ta zargi kotun majistare da ci gaba da bayar da umarnin kama su, wanda hakan a cewarta ya saɓa doka.

Gwamna Dauda Lawal
Dattawan Zamfara sun zargi Gwamna Dauda da hana 'yan majalisa sakewa Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Wace shawara aka ba Gwamna Dauda?

Ƙungiyar ta buƙaci Gwamna Dauda Lawal da ya dakatar da muzguna musu sannan ya nemi zaman sulhu da ƴan majalisar domin warware rikicin cikin lumana.

"Jam’iyyar APC za ta ci gaba da tsayawa kan doka, kuma ba za ta lamunci amfani da kotu domin cimma manufar siyasa ba."
"Mun jajirce wajen ƙin yarda da duk wani yunkuri na razana ƴan majalisa saboda suna magana kan taɓarɓarewar tsaro a yankunansu, matsalar da gwamnatin jihar ta kasa magancewa."

- Dr. Abdulmumin Kamil Gusau

Gwamna Dauda ya musanta shirin barin PDP

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi magana kan jita-jitar da ake yaɗawa mai cewa zai bar jam'iyyar PDP.

Kara karanta wannan

Hadakar Atiku ta fara gigita APC, an fallasa abin da Tinubu ke kullawa 'yan adawa

Gwamna Dauda Lawal ya ƙaryata jita-jitar inda ya ce ko kaɗan babu ƙamshin gaskiya a cikinta.

Ya ba da tabbacin cewa shi cikakken mamba ne a PDP kuma sannan zai ci gaba da kasancewa a cikinta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng