Gwamnoni 19 Sun Yi Maganar Rasuwar Babban Malami, Sheikh Idris Dutsen Tanshi

Gwamnoni 19 Sun Yi Maganar Rasuwar Babban Malami, Sheikh Idris Dutsen Tanshi

  • A madadin gwamnonin jihohin Arewa 19, Gwamna Inuwa Yahaya na jihar Gombe ya yi ta'aziyyar rasuwar Sheikh Idris Abdul'Aziz Dutsen Tanshi
  • Shugaban ƙungiyar gwamnonin Arewa ya ce labarin rasuwar malamin ya girgiza shi domin rashi ne da ya shafi ɗaukacin al'ummar musulmi
  • Gwamna Inuwa Yahaya ya roki Allah SWT ya gafarta wa Sheikh Idris Dutsen Tanshi, ya masa rahama, kuma Ya bai wa iyalansa haƙuri

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Gombe - Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi alhinin rasuwar Sheikh Idris Abdul'Aziz Dutsen Tanshi.

Gwamna Inuwa ya miƙa sakon ta'aziyya bisa rasuwar fitaccen malamin addinin musulunci na Bauchi, wanda ya koma ga Allah a daren Juma'a.

Gwamna Inuwa Yahaya.
Gwamna Inuwa Yahaya ya yi jimamin rasuwar Dr. Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi Hoto: Muhammad Inuwa Yahaya
Asali: Facebook

Daily Trust ta tattaro cewa marigayin ya rasu a garin Bauchi bayan fama da jinya ta tsawon lokaci wanda ta kai ga dakatar da karatuttukansa.

Kara karanta wannan

"Mutane sun manta": Tinubu ya faɗi aikin da Sheikh Dutsen Tanshi ya yi wa Najeriya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An yi jana'izar babban malamin na sunnah da misalin karfe 10:00 na safiyar yau Juma'a, 4 ga watan Afrilu, 2025 a jihar Bauchi da ke Arewa maso Gabas.

Gwamna ya yi alhinin rashin Dr. Dutsen Tanshi

Da yake ta'aziyyar rasuwar, Gwamna Inuwar Yahaya ya yi alhinin wannan rashi da muaulmi suka yi.

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Gombe, Isma'ila Uba Misilli ya fitar da yammacin tau Juma'a.

Gwamna Inuwa Yahaya ya ce ya girgiza da ya samu labarin rasuwar malamin mara daɗi kuma abin takaici da jimami.

A cewarsa, Dr. Dutsen Tanshi malami ne mai ƙima kuma babban mai wa’azi, wanda ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen yaɗa ilimin addini da kuma tarbiyyar al’umma da kyawawan halaye.

Gwamnoni 19 sun yi ta'aziyyar Dutsen Tanshi

Gwamnan ya ƙara da cewa wannan rashi ba na iyalansa da mutanen jihar Bauchi kaɗai ba ne, rashi ne da ya taɓa duk wasu ɗaliban addini da ke amfana da ilimin marigayin.

Kara karanta wannan

Abin da malaman Musulunci ke fada game da rasuwar Sheikh Idris Dutsen Tanshi

“A madadin jama'a da gwamnatin jihar Gombe, da kuma gwamnonin jihohi 19 na Arewacin Najeriya, ina miƙa ta’aziyya ga iyalan marigayin, gwamnatin Bauchi, da daukacin al’ummar Musulmi.”

- In ji Inuwa Yahaya.

Inuwa Yahaya.
Gwamnoni 19 yi jimamin rasuwar Dr. Idris Dutsen Tanshi Hoto: Muhammad Inuwa Yahaya
Asali: Facebook

Gwamna Inuwa Yahaya ya roƙi Allah Madaukakin Sarki da Ya gafarta wa Dr. Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi, Ya sanya shi cikin Aljannar Firdaus.

Shugaban gwamnonin Arewan ya kuma roƙi Allah SWT Ya bai wa iyalansa da masoyansa juriyar da za su iya jure wannan babban rashi.

Tinubu ya yi alhinin rasuwar Dutsen Tanshi

A wani rahoton, kun ji cewa shugaban ƙasa, Bola Tinubu ya yi ta'aziyyar rasuwar shahararren malamin musuluncin nan, Sheikh Idris Abdul'Aziz Dutsen Tanshi.

Tinubu ya yabi marigayi Dutsen Tanshi bisa gudummuwar da ya bayar wajen yaki da tsattsauran ra'ayi na ƴan Boko Haram a yankin Arewa maso Gabas tun farko.

Shugaban ƙasa ya yi addu’a Allah ya jikansa, sannan ya roƙi iyalansa, almajiransa, da masoyansa su yi haƙuri da wannan rashi.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng

iiq_pixel