Fadar Sarkin Musulmi Ta Faɗi Dalilin da Ya Sa Take Amfani da Ganin Watan Saudiyya a Najeriya
- Kwamitin ganin wata na faɗar sarkin Musulmi ya yi bayanin yadda ake tantance ganin wata ko da ilimi ya nuna ba za a gan shi ba a Najeriya
- Malam Simwal Usman ya sake nanatawa cewa a ilimin falaki dai ba za a ga watan sallah ranar Asabar watau 29 ga watan Ramadan ba
- Amma ya ce idan an gan shi a kasashe kamar Saudiyya, kwamitin fatawa na fadar sarkin kan ba da fatawar za a iya amfani da ganinsu
CHECK OUT: Education is Your Right! Don’t Let Social Norms Hold You Back. Learn Online with LEGIT. Enroll Now!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Sokoto - Ɗaya daga cikin ƴan kwamitin ganin wata na fadar sarkin Musulmi, Simwal Usman Jibrin ya bayyana yadda ake duban wata da tantancewa kafin a sanar a Najeriya.
Masanin ilimin taurarin ya ce idan kwamitin ganin wata ya tattara rahotannin da ya samu, ya na miƙawa sarkin musulmi ne domin yanke hukuncin ƙarshe.

Kara karanta wannan
Azumi 30: Abin da ya sa ba zai yiwu a ga jinjirin watan Shawwal a ranar Asabar ba

Asali: Facebook
Malam Simwal ya yi wannan bayani a wata hira da DCL Hausa ta yi da shi kan yiwuwar ganin jinjirin watan Shawwal ranar Asabar, 29 ga watan Ramadan.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Za a ga wata ranar Asabar a Najeriya?
Simwal ya bayyana cewa a bincikensu na masana, sun tabbatar da cewa ba za a ga wata ranar Asabar ba.
A cewarsa, za a samar da watan ne da misalin karfe 11:58 na safiya a ranar Asabar, wanda ke nuna zuwa faɗuwar rana watan ba zai wuce awanni 6 da mintuna 40 ba.
Ya jaddada cewa a ilimin falaki, ba za a iya ganin watan da bai wuce awanni 6 da minti 40 ba da ƙwayar ido, don haka a ganinsu ba za a ga wata ba ranar Asabar.
Simwal ya ƙara da cewa ko da ilimi ya nuna ba za a ga wata ba, za a iya samun waɗanda za su ce sun ga wata ko kuma ƙasashen gabas kamar Saudiyya su gani.
Sarkin musulmi na ɗaukar ganin watan Saudiyya?
Ya ce idan irin haka ta faru, kwamiti kan miƙa rahoto ga sarkin Musulmi shi kuma ya nemi shawara daga kwamitin fatawa karkashin jagorancin Sheikh Sharif Saleh.
"A a gaskiya a ilimance ba za a gan shi ba, amma ire-iren wannan ta faru kuma za ka ji wasu sun ce sun ganshi ko ƙasashen gabas su ce sun ganshi.
"Abin da Mai alfarma sarkin musulmi yake yi shi ne ya tuntuɓi kwamitin fatawa karkashin jagorancin Sheikh Sharif Saleh, su ake ba damar yin fatawa shin za a amshi ganin nan ko kuwa."
"Wani lokacin suna ba da fatawar cewa tun da ƙasashen gabas sun gan shi kamar Saudiyya, magabata sun ce idan ƙasashen da ke gabas da ku sun gan shi to za ku iya amfani da shi.
- In ji Simwal.

Asali: Twitter
Sarkin Musulmi ke yanke shawara ta karshe
Masanin ya tabbatar da cewa sarkin Musulmi ke yanke shawara da kwamitin fatawa kan amsar ganin wata duk da ilimin falaki ya ce ba za a ganshi ba.
Ya musanta zargin cewa kwamitin ganin wata na bin duk abin da Saudiyya ta sanar, ya na mai cewa a ilimi, duk watan da aka gani a can za a iya ganinsa a Najeriya.
"Watan nan guda ɗaya ne kuma banbancin lokacinmu da Saudiyya awa biyu ne kacal, don haka har in za a iya ganin wata a Saudiyya to za a ganshi a Najeriya."
Yaushe za a yi sallah a Saudiyya?
A wani labarin, kun ji cewa ƙasashen gabas kamar Saudiyya da Qatar sun fara shirin fita duban watan karamar sallah ranar Asabar, 29 ga watan Ramadan.
Hasashen ya bayyana ranakun da ake kyautata zaton waɗannan ƙasashe za su yi sallah a bana bayan kammala azumi 29 ko 30.
Asali: Legit.ng