Ana Batun Cin Zarafin Sanata, Remi Tinubu Ta Bukaci Karin Wakilcin Mata a Majalisa

Ana Batun Cin Zarafin Sanata, Remi Tinubu Ta Bukaci Karin Wakilcin Mata a Majalisa

  • Sanata Oluremi Tinubu ta jaddada muhimmancin ware kujeru na musamman ga mata a majalisar dokoki da mukaman zartarwa
  • Ta ce mata na taka muhimmiyar rawa a ci gaban kasa, don haka yana da muhimmanci a ba su karin dama a siyasa da shugabanci
  • Uwargidan shugaban kasar ta fadi haka ne don nuna goyon baya ga kudirin da zai ware 35% na kujerun majalisun jihohi da tarayya ga mata

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT AbujaUwargidan Shugaban Kasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta bayyana goyon bayanta ga kudirin dokar da ke neman ware kujeru na musamman ga mata a majalisar dokoki.

Kudirin, wanda Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Okezie Kalu, ya dauki nauyin gabatarwa, yana kan matakin nazari a halin yanzu.

Kara karanta wannan

Zargin lalata: Sanata Natasha na tsaka mai wuya, Hadimin Osinbajo ya tona shirin majalisa

Tinubu
Uwargidan Tinubu na son a kara yawan kujerun mata a majalisa Hoto: Senator Oluremi Tinubu
Asali: Facebook

Daily Trust ta wallafa cewa an gabatar da irin wannan kudiri a Majalisar Tarayya ta Tara ta hannun tsohuwar ‘yar majalisa, Nkeiruka Onyejeocha, amma bai samu nasarar wucewa ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanata Oluremi Tinubu, wacce ta jaddada muhimmancin kudirin ta kuma kara da yin kira ga Majalisar Tarayya da ta gaggauta amincewa da shi.

"A kara yawan mata a majalisa," Remi Tinubu

The Nation ta ruwaito cewa Uwargidan Shugaban Kasa, wacce Hajiya Fatima Tajudeen Abbas, matar Kakakin Majalisar Wakilai, ta wakilta ta nanata goyon bayanta ga kudirin a wani taro a Abuja.

Ta ce:

"Ya na da matukar muhimmanci a mai da hankali kan bukatar karin wakilcin mata a matsayi na jagoranci da yanke shawarwari a kan abinda ya shafi jama'arsu.
Mata na da matukar muhimmanci a ci gaban kasarmu, amma har yanzu an takaita wakilcin jama'arsu da suke yi a wani mataki.”

Uwargidan shugaban kasar ta sake tabbatar da goyon bayanta ga kudirin, wanda ke bukatar a ware akalla 35% na kujerun majalisa da mukaman zartarwa ga mata.

Kara karanta wannan

El Rufa'i: Kotu ta umarci ICPC ta kwato sama da N1bn da aka karkatar a Kaduna

Remi Tinubu: "Mata na da muhimmanci"

Sanata Remi Tinubu ta ce mata suna da matukar muhimmanci a wajen zartar da manufofin da suka shafi kasa, saboda haka bai kamata a dakile su ba.

Tinubu
Sanata Oluremi Tinubu ta ce mata suna da muhimmanci a shugabanci Hoto: Senator Oluremi Tinubu
Asali: Facebook

Ta ce:

"Saboda haka, ina goyon bayan kudirin da ke bukatar a ware akalla 35% na kujerun majalisa da mukaman zartarwa ga mata.
Ina kuma kira ga Majalisar Tarayya da ta gaggauta amincewa da wannan kudiri. Ni a shirye nake na mara baya ga duk wata manufa da za ta inganta wakilcin mata da gina kasa.”

An yi takaicin karancin mata a shugabanci

A nasa bangaren, Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu, wanda ke jagorantar kudirin, ya nuna damuwa kan yadda mata ke fuskantar karancin wakilci a shugabanci.

Kudirin na da nufin gyara kundin tsarin mulkin 1999 domin ware kujeru na musamman ga mata a majalisun dokokin jihohi da na kasa baki daya.

Ministar Harkokin Mata, Hajiya Imman Suleiman, tare da wasu manyan baki, sun bayyana cikakken goyon bayansu ga wannan kudiri tare da bukatar a amince da shi cikin gaggawa.

Kara karanta wannan

Dalibai sun fusata kan rufe makarantu a Arewa, NANS ta shirya zanga-zanga

Remi Tinubu ta yi rabon kudi a Arewa

A wani labarin, kun ji cewa Uwargidan Shugaban Kasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta kaddamar da rabon tallafin Naira miliyan 50 ga tsofaffi 250 daga jihohin Nasarawa da Gombe.

A jihar Nasarawa, an gudanar da taron rabon tallafin a birnin Lafia, inda aka kara yawan kudin tallafin daga N100,000 zuwa N200,000 domin kara rage radadin matsin tattalin arziki.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.

Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng