Yadda Sanatoci Suka Jawo Hankalin Tinubu Ya Waiwayi Gyaran Titunan Arewa

Yadda Sanatoci Suka Jawo Hankalin Tinubu Ya Waiwayi Gyaran Titunan Arewa

A 'yan kwanakin nan, an samu korafe korafe daga yankin Arewacin Najeriya a kan tituna da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu za ta kashe N4.2tn wajen gyarawa.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - Gwamnatin tarayya ta amince da sabunta wasu tituna a yankuna daban daban na kasar nan, inda aka ware N4.2tn.

Sanata mai wakiltar Gombe ta Tsakiya, Muhammad Danjuma Goje ya yi korafi a zauren majalisar kan cewa Arewa maso Gabas bai samu wakilci yadda ya kamata ba a kudin da aka ware.

Sanata Goje
Sanata Goje ya bukaci gyara titunan Arewa maso Gabas. Hoto: Bayo Onanuga|Muhammad Adamu Yayari
Asali: Facebook

A wannan rahoton, mun tattaro muku jerin titunan da gwamnatin tarayya za ta gyara da yadda shugabannin yankuna suka yi korafi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hanyoyin da gwamnatin tarayya za ta gyara

A wani taron Majalisar Zartarwa ta Kasa da aka gudanar, ministan ayyuka, Dave Umahi, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta amince da ware kudi domin gyaran wasu hanyoyi 14.

Kara karanta wannan

Matashi ya gayyaci abokinsa gida ya masa kisan wulakanci da adda, ya sassara shi

Daily Trust ta wallafa cewa Ministan ya ce matakin na cikin shirin gwamnatin Tinubu na sake dubi, tsari da kuma fifita manyan ayyukan da aka gada daga gwamnatocin baya.

Rahotanni sun nuna cewa daga cikin hanyoyin da za a gyara akwai titin Kaduna-Jos wanda za a kashe Naira biliyan 33.42.

Aikin titi
Yadda ma'aikata ke gyaran titi. Hoto: Kola Sulaimon
Asali: Getty Images

Hakanan akwai titin Agaye-Kachia-Baro a jihar Neja da za a kashe Naira biliyan 22 a kansa, da titin Odukpani Junction–Apeti a jihar Kuros Riba wanda kudinsa ya kai Naira biliyan 26.33.

Sauran titunan sun hada da:

  • Titin Abeokuta-Ajibo zuwa Iyana Mosa a jihar Ogun – Naira Biliyan 10.89
  • Titin Umuahia-Ikuano-Ikot Ekpene a jihar Abia – Naira Biliyan 14.37
  • Titin Yola-Fufore-Gurin a jihar Adamawa – Naira Biliyan 11.81
  • Titin Ikorodu-Shagamu a jihar Legas – Naira Biliyan 27.59
  • Titin Nkomoro-Isu a jihohin Enugu da Ebonyi – Naira Biliyan 14.49

Kara karanta wannan

"Bai dace gwamnati ta nade hannayenta ba": Ndume ya nemi majalisa ta duba zargi kan USAID

Korafin Sanata Goje ga Shugaba Tinubu

Sanata Danjuma Goje, wanda tsohon gwamnan Jihar Gombe ne, ya nuna damuwa kan yadda yankin Arewa maso Gabas bai samu kaso mai yawa ba a cikin aikin titunan da za a yi.

A cewar Sanata Goje, yankin ya samu ayyuka biyu ne kacal:

  • Titin Yola – Fufore – Gurin a Jihar Adamawa
  • Titin Karim Lamido a Jihar Taraba

Ya kara da cewa kudin da aka ware domin yin titunan a jimillar kudin bai kai ko kashi daya bisa goma na N4.2tn da aka ware ba.

Sanata Goje
Sanata Goje a majalisar dattawa. Hoto: Muhammad Adamu Yayari
Asali: Twitter

Danjuma Goje ya lissafo wasu muhimman hanyoyin yankin da ke bukatar gyaran gaggawa, irin su:

  • Titin Bauchi – Gombe
  • Titin Potiskum – Gombe
  • Titin Yola – Mubi
  • Titin Biu – Damboa –
  • Titin Maiduguri – Numan – Jalingo

Majalisa ta goyi bayan Sanata Goje

Duk da cewa Sanata Goje ne ya gabatar da kudirin, ‘yan majalisa da dama sun nuna goyon bayansu, inda suka bayyana yadda lalacewar hanyoyi ke shafar tattalin arzikin yankin.

Kara karanta wannan

Tinubu ya ba da umarni a dauki ma'aikatan lafiya 150 aiki, an ji inda za a tura su

Sanata Tahir Monguno daga Borno ya bayyana cewa yankin Arewa maso Gabas ne yafi kowa fuskantar koma baya a bangaren abubuwan more rayuwa.

Sanata Munguno
Sanata Ali Ndume da Tahir Monguno. Hoto: Ali Ndume|Nigerian Senate
Asali: Twitter

Sanata Munguno ya ce rashin wadannan hanyoyi na hana kasuwanci bunkasa, musamman a yankunan da rikicin Boko Haram ya yi wa illa.

Jaridar Premium Times ta wallafa cewa biyo bayan korafin, majalisar dattawa ta yi kira ga gwamnatin tarayya ta sanya karin tituna a Arewa maso Gabas cikin ayyukan.

Sanata Sani Musa ya yi korafi

Sanata Sani Musa daga Niger ya bukaci a gayyaci Ministan Ayyuka, David Umahi ya yi bayani kan dalilin da ya sa har yanzu manyan tituna ke lalace duk da kudin SUKUK da ake warewa.

Ya ce yana da muhimmanci a binciki yadda ake tafiyar da kudin gyaran hanyoyi domin gujewa sake fadawa irin wannan matsala a nan gaba.

Sani Musa
Sanata Sani Musa yana bayani a majalisar dattawa. Hoto: Senator Mohammed Sani Musa
Asali: Facebook

Sanata Musa ya bayyana cewa kasafin kudin 2025 ya ware Naira tiriliyan 4.3 don ayyukan hanyoyi, amma Jihar Neja ta samu aiki guda daya ne kawai, wato titin Agaie-Katcha-Baro.

Kara karanta wannan

An kaddamar da shirin karban tuban 'yan bindiga da koya musu sana'o'i

Duk da haka Sanata Sani Musa ya wallafa a Facebook cewa titin ma an ware masa kasa da rabin Naira biliyan 1 ne kawai.

A karkashin haka ya ce akwai hanyoyi masu cunkoson jama'a a jihar Neja da suke bukatar kulawar gwamnatin Bola Tinubu wajen sabunta su.

Jingir ya jawo hankalin Tinubu

A wani rahoton, kun ji cewa Sheikh Sani Yahaya Jingir ya ce shi ya jawo hankalin gwamnatin Bola Tinubu kan gyara titin Kaduna-Jos.

Malamin ya ce ya jawo hankalin gwamnatin ne da ya gayyaci al'umma ya kafa gidauniyar gyara titin da ya shafe shekaru yana lalace.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng