Gobara Ta Tashi a Ofishin Hukumar INEC, Ta Jawo Gagarumar Barna

Gobara Ta Tashi a Ofishin Hukumar INEC, Ta Jawo Gagarumar Barna

  • An samu tashin gobara a ofishin hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) da ke jihar Sokoto yayin da ake fama da hazo
  • Gobarar wacce ta tashi a ofishin hukumar na ƙaramar hukumar Gwadabawa ta lalata kayayyakin zaɓe masu yawan gaske
  • Hukumar INEC ta bayyana cewa an fara gudanar da bincike domin gano musabbabin tashin gobarar wacce ta lalata ginin ofishin

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Sokoto - An samu tashin wata gobara a ofishin hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) da ke jihar Sokoto.

Gobarar ta tashi ne a ofishin hukumar INEC da ke ƙaramar hukumar Gwadabawa, a jihar Sokoto.

Gobara ta tashi a ofishin INEC a Sokoto
Gobara ta lalata kayayyaki a ofishin hukumar INEC da ke Sokoto Hoto: INEC Nigeria
Asali: Twitter

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan INEC na ƙasa, Sam Olumekun, ya fitar a shafin X hukumar.

Kara karanta wannan

Mutanen gari sun firgita da cewa 'Allah ya yi wahayi' makiyaya za su kai hari

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gobara ta tashi a ofishin hukumar INEC

Gobarar ta lalata aƙalla akwatunan zaɓe 558 da sauran kayayyakin zaɓe.

Sam Olumekun ya bayyana cewa gobarar na iya kasancewa sakamakon wutar lantarki mai ƙarfi da aka kawo a yankin.

"Gobarar ta tashi da sassafe a ranar Talata, 11 ga watan Fabrairu, 2025, inda ta yi mummunar ɓarna ga dukkan ginin ofishin."
“Kayayyakin da gobarar ta lalata sun haɗa da kujeru da tebura, da kuma kayan zaɓe ciki har da akwatunan zaɓe 558, wuraren kaɗa ƙuri'a 186, jakunkunan zaɓe 186."
"Sauran sun haɗa da tankunan ruwa 12 (masu cin lita 1,000), katifu 400 da bokitai 300."
"Jami'an tsaro da hukumomin kiyaye gobara da suka tura jami'ansu zuwa ofishin na ci gaba da binciken musabbabin tashin gobarar."
"Ba a samu raunuka ko asarar rai ba a yayin tashin gobarar."

- Sam Olumekun

Gobara ta yi ɓarna a ofishin INEC

Ya bayyana cewa gobarar ta yi ɓarna sosai ga ofishin, lamarin da zai iya tasiri a shirye-shiryen zaɓe a yankin.

Kara karanta wannan

"An zuba wa INEC ido ta na sha'aninta," Makusancin Kwankwaso ya dira kan hukumar zabe

Hukumar INEC ta bayyana cewa tana ƙoƙarin duba yiwuwar maye gurbin kayayyakin da suka lalace domin tabbatar da cewa shirye-shiryen gudanar da zaɓe ba su samu cikas ba.

INEC ta dura kan Hudu-Ari

A wani labarin kuma, kun ji cewa hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta dura a kan korarren kwamishinan zaɓenta na jihar Adamawa, Yunusa Hudu-Ari.

Hukumar INEC ta buƙaci korarren kwamishinan da ya je kotu ya kare kansa kan tuhume-tuhumen da ake yi masa na aikata ba daidai ba lokacin zaben 2023.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng