Dan Majalisa daga Arewa Ya Fadi Gyaran da Ya Kamata a Yi Wa Kudirin Haraji

Dan Majalisa daga Arewa Ya Fadi Gyaran da Ya Kamata a Yi Wa Kudirin Haraji

  • Ɗan majalisar wakilai daga jihar Borno, Ahmed Jaha ya taɓo batun ƙudirin haraji da ke gaban majalisa
  • Ahmed Jaha wanda ke wakiltar Gwoza da Damboa ya bayyana cewa akwai sassa daban-daban na ƙudirin waɗanda ke buƙatar a yi musu gyara
  • Ɗan majalisar ya nuna adawarsa kan harajin gado da ke cikin ƙudirin, inda ya ce ya saɓawa koyarwar addinan ƙasar nan

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Ɗan majalisar wakilai da ke wakiltar Chibok da Damboa daga jihar Borno, Hon. Ahmed Jaha, ya yi magana kan ƙudirin harajin gwamnatin Bola Tinubu.

Ɗan majalisar ya bayyana cewa ya nuna damuwa kan wasu sassa na ƙudirin gyaran harajin saboda akwai wuraren da suke buƙatar a yi musu gyara.

Dan majalisar Borno ya yi magana kan kudirin haraji
Dan majalisa daga Borno ya yi magana kan yin gyara a kudirin haraji Hoto: @HouseNGR, @OfficialABAT
Asali: Facebook

Jaridar Vanguard ta rahoto cewa ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da manema labarai a birnin tarayya Abuja.

Kara karanta wannan

Duk da yin sulhu, 'yan.bindiga sun tafka ta'asa a jihar Kaduna

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Me ɗan majalisar ya ce kan ƙudirin haraji?

A cewarsa, tun da farko an nuna damuwa kan ƙuɗirin lokacin da aka gabatar da shi a gaban majalisa saboda yadda ɓangaren zartaswa ya kawo shi.

"Da farko dai, an tura ƙudirin ne duk da ƙin amincewa da shi da majalisar tattalin arziƙi ta ƙasa ta yi."
"Haka kuma dattawan ƙasar nan sun ƙi amincewa da shi, sannan gwamnonin jihohi, musamman na Arewa, sun nuna rashin amincewarsu kan ƙudirin."

- Hon. Ahmed Jaha

Dalili na biyu a cewar sa shi ne bayan nazari kan ƙudirin, ƴan majalisa sun fahimci cewa akwai wasu sassa da ke buƙatar a sake duba su domin tabbatar da adalci da kyakkyawan shugabanci.

"Wannan ne dalilin da ya sa ƙudirin ya jawo ce-ce-ku-ce tun farko. A wasu lokuta, ƴan majalisa su kan cimma matsaya ɗaya idan buƙatar hakan ta taso, amma a kan wannan ƙudiri, mun samu rarrabuwar kai tun daga farko."

Kara karanta wannan

Gwamnatin Zamfara ta sake fayyace matsayarta kan sulhu da 'yan bindiga

- Hon. Ahmed Jaha

Ɗan majalisa ya hango gyara a ƙudirin haraji

Ya kuma bayyana adawarsa da harajin gado da aka saka a cikin ƙudirin, yana mai cewa hakan ya saɓawa koyarwar addinin Musulunci, Kiristanci da sauran addinai.

A cewarsa, addinin Musulunci ya yi bayani ƙarara cewa ba a yarda a taɓa dukiyar wanda ya rasu ba.

"Ko a addinin Kiristanci, ko a Musulunci, ko ma a addinin gargajiya, ana kiyayewa tare da kare haƙƙin gadon mamaci."
"Musamman a addinin Musulunci, ba a yarda ko ruwa ka siya daga kuɗin gado ka ba wani wanda ba ya da haƙƙi ko ikon samun wannan gadon."
"Don haka batun cire haraji daga abin da mamaci ya bari ya sabawa koyarwar Musulunci. Kuma ina da yaƙinin cewa hakan ya saba da al’adu da dokokin wasu addinai da dama."

- Hon. Ahmed Jaha

Ɗan majalisa ya soki ƙudirin haraji

A wani labarin kuma, kun ji cewa wani ɗan majalisar wakilai daga jihar Katsina, Sada Soli ya nuna cewa akwai kura-kurai a cikin ƙudirin haraji.

Kara karanta wannan

Shahararrun 'yan bindiga sun tuba, sun mika makamansu ga jami'an tsaro

Ɗan majalisar mai wakiltar Jibia/Kaita ya bayyana cewa an ba shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu gurguwar shawara kan ƙudirin harajin.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng

iiq_pixel