Gwamnati Ta Rushe Makarantun Sakandare, Ta Kawo Sabon Tsarin Ilimi a Najeriya

Gwamnati Ta Rushe Makarantun Sakandare, Ta Kawo Sabon Tsarin Ilimi a Najeriya

  • Gwamnatin ta gabatar da tsarin karatun bai daya na shekaru 12, wanda zai kawo karshen tsarin karatun sakandare na JSS, SSS
  • Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ya bayyana cewa wannan tsarin zai rage yawan daliban da ke fita daga makaranta da inganta ilimi
  • Gwamnatin tarayyar ta ce sabon tsarin zai kawo cigaba mai dorewa a fannin ilimi, wanda ake sa ran zai dace da bukatun duniya

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Gwamnatin tarayya ta sanar da soke dukkanin kananan makarantun sakandare (JSS) da manyan makarantun sakandare (SSS) na kasar nan.

Gwamnatin ta gabatar da sabon tsarin karatun bai daya na shekaru 12, wanda zai bai wa yara damar neman ilimin firamare da sakandare a hade.

Ministan ilimi ya yi magana da gwamnati ta canja tsarin ilimi a Najeriya
Gwamnati ta rushe manya da kananan makarantun sakadanre, ta kawo sabon tsari. Hoto: Audu Marte
Source: Getty Images

Gwamnati ta canja tsarin ilimi a Najeriya

Wannan cigaba yana nufin gwamnatin Najeriya na neman kawar da tsarin ilimin 6-3-3-4, sannan ta maye gurbin sa da tsarin 12-4, inji rahoton The Guardian.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Kano ta kashe sama da N1.5bn a gina mayanka a kananan hukumomi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Haka kuma, an nemi majalisar kolin ilimi ta kasa (NCE) ta amince da shekaru 16 a matsayin mafi ƙanƙantar shekarun shiga jami’o’i a kasar.

Ministan ilimi, Dakta Tunji Alausa, ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis, 6 ga watan Fabrairu, 2025, a Abuja, yayin taron gaggawa na NCE.

Minista ya yi magana a taron NCE

Rahoto ya nuna cewa NCE ita ce hukuma mafi girma da ke yanke shawara a bangaren ilimi a Najeriya.

A wajen taron, an samu halartar kwamishinonin ilimi daga jihohi 36 da babban birnin tarayya (FCT), hukumomi, da kungiyoyi.

A cewar Dakta Alausa, idan an haɗa ilimin sakandare cikin ilimin bai daya, dalibai za su samu damar ci gaba da karatu ba tare da katsewa ba har zuwa shekaru 16.

Gwamnati ta fadi manufar canja tsarin ilimin

Ministan ilimin kasar ya ce sabon tsarin yana cikin sababbin hanyoyin ilimi da ake amfani da su a duniya a wannan zamanin.

Kara karanta wannan

"Akwai matsala": Majalisar amintattun PDP ta shiga taron gaggawa a Abuja

Ya ƙara da cewa wannan gyaran zai rage yawan daliban da ke fita daga makaranta saboda matsalolin kudi da tsarin da ke hana su kammala karatu.

“Wannan tsarin zai tabbatar da samun manhajar karatu guda daya wacce za a aiwatar a dukkanin sassan kasar,” inji Alausa.

Ministan ya kuma ce idan ya zamana dalibai suna shafe shekaru 12 kafin shiga jami'a, da shekaru 4 a jami'a, za su samu kwarewar sana'o'i da kirkire-kirkire.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com