"Zargin Baki Biyu": Fusatattun Mutane Sun Bankawa Gidan Basarake Wuta a Jihar Kano

"Zargin Baki Biyu": Fusatattun Mutane Sun Bankawa Gidan Basarake Wuta a Jihar Kano

  • Fusatattun mutane sun ƙone gidan Mai Gari a kauyen Rimin Zakara da ke ƙaramar hukumar Ungogo a jihar Ƙano
  • Rigima ta kaure a garin ne sakamakom rushe gine-ginen jama'a da hukumomin gwamnati suka yi, wanda ya fusata mazauna yankin
  • Har kawo yanzu babu wata sanarwa a hukumance kan ƙone gidan basaraken amma ana tsammanin tuni hukumomin tsaro suka fara ɗaukar matakai

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - A daren Lahadi, wasu fusatattun mutane sun cinna wa gidan Mai Garin kauyen Rimin Zakara wuta bayan rikici ya ɓarke tsakanin jami’an tsaro da mazauna yankin.

Wannan tashin hankali ya biyo bayan yunkurin rushe gine-gine da ake zargin an yi su ba bisa ƙa’ida ba a yankin, wanda hakan ya haddasa ce-ce-ku-ce tsakanin jama’a da mahukunta.

Taswirar Kano.
Fusatattun matasa sun banka wa gidan Magajin Gari wuta a Kano Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Abin da ya haddasa rigima a Kano

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun shiga gari gari, sun kashe bayin Allah duk da gwamna ya yi sulhu da su

Rahoton Aminiya ya nuna cewa rigimar ta samo asali ne daga matakin da jami’an Hukumar Tsara Birane ta Kano (KNUPDA) suka ɗauka na rushe gine-ginen da ke kusa da filin Jami’ar Bayero.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mazauna yankin, waɗanda suka fusata da wannan mataki, sun fito domin nuna adawa da rushe gidajensu.

Majiyoyi da dama daga yankin sun nuna cewa galibin gidajen da aka rusa hukumar KNUPDA ta shafa masu fenti, alamar da ke nuna aiki zai biyo ta kansu.

Sai dai hakan ya jawo arangama da jami’an tsaro, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane huɗu.

Mutane sun ƙona gidan basarake

Bayan aukuwar wannan tashin hankali, wasu da ba a san ko su waye ba sun fantsama gidan Mai Garin suka cinna masa wuta, wanda ya ƙone kurmus.

An ruwaito cewa Mai Garin da sauran iyalansa sun tsere domin tsira da rayuwarsu.

Wasu shaidu sun bayyana cewa ana ganin kona gidan mai garin a matsayin martani kan yadda aka rushe gine-ginen ba tare da sassauci ba.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun tare matafiya, sun yi awon gaba da fasinjoji zuwa daji

Hukumomi dai har yanzu ba su fitar da cikakken bayani kan lamarin ba, amma ana sa ran za a gudanar da bincike don gano hakikanin dalilin kona gidan mai garin da kuma matakan da za a ɗauka kan hakan.

Kotu ta yankewa mutum 5 hukuncin kisa

A wani labarin, kun ji cewa kotun Kano ta yanke mutum biyar hukuncin kisa ta hanyar rataya bisa kama su da laifin kashe wata mata da suka kira mayya.

Wadanda ake tuhuma sun rutsa matar a gonarta da ke garin Dadin Kowa a ƙaramar hukumar Wudil, suka daba mata wuka har ta mutu.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

iiq_pixel