'Hukuncin da Ya Kamaci Masu Cin Hanci': Inji Yaron Buhari duk da Zargin Rashawa a Lokacinsu

'Hukuncin da Ya Kamaci Masu Cin Hanci': Inji Yaron Buhari duk da Zargin Rashawa a Lokacinsu

  • Tsohon mai ba da shawara ga Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bukaci a aiwatar da hukuncin kisa ga masu cin hanci da rashawa a Najeriya
  • Obono Obla ya ce wannan mataki mai tsauri zai hana mutane aikata rashawa, wanda ke kawo cikas ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewa
  • Obla ya jaddada bukatar inganta hukumomi, inganta gaskiya da rikon amana, tare da hukunta masu aikata laifuffukan rashawa don gyara al'umma

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Tsohon hadimin ga Muhammadu Buhari ya yi bukaci gurfanarwa da hukuncin kisa ga masu cin hanci da rashawa.

Okoi Obono Obla, ya ba shawarar daukar matakin ne mai tsauri saboda daidaita lamura a Najeriya da samar da ci gaba.

Tsohon hadimin Buhari ya ba da shawara kan masu cin hanci da rashawa
Tsohon hadimin Buhari ya bukaci hukuncin kisa kan masu cin hanci a Najeriya. Hoto: Obono Obla, Muhammadu Buhari.
Asali: Facebook

Cin hanci: Tsohon hadimin Buhari ya kawo mafita

Kara karanta wannan

Yadda 'yan Najeriya ke buya a Amurka bayan Trump ya zafafa dokoki

Obla bayyana hakan a Calabar yayin jawabinsa a taron tunawa da Ralph Opara karo na 16, wanda Kungiyar NAS ta shirya, cewar The Guardian.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tsohon hadimin ya ce hakan na daya daga cikin hanyoyin dakile cin hanci da rashawa da ya yi katutu a kasar.

"Daya daga cikin hanyoyin da za a iya dauka shi ne kafa dokar hukuncin kisa ga wasu nau’ukan cin hanci da laifuffukan kudi.”
“Wannan mataki mai tsauri na iya zama wata hanya ta dakile masu aikata rashawa, don rage illa da wannan dabi’a ke haifarwa a cikin al’umma.”

- Obono Obla

Yadda cin hanci ke hana ci gaban kasa

Obla ya bayyana yadda wasu ‘yan Najeriya ke kokarin kare muradun kasa, yayin da wasu ke cin hanci da rashawa wanda ke hana ci gaba.

Ya jaddada bukatar inganta hukumomi, karfafa gaskiya da rikon amana, tare da tabbatar da cewa masu laifi sun fuskanci hukunci.

Kara karanta wannan

Tsohon sanata ya zubar da hawaye da kotu ta yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru 11

Haka kuma, ya ce akwai bukatar sake duba dabi’un al’umma da ci gaban tunani don magance tushen matsalar rashawa.

Ya kara da cewa dole ne kungiyoyin masu zaman kansu da na farar hula da gwamnati su hada kai wajen gina al'umma mai gaskiya da rikon amana.

Shawarar shugaban kungiyar NAS a Najeriya

A nasa bangaren, Shugaban NAS, Dr. Joseph Oteri, ya ce taron an shirya shi ne don tunawa da Ralph Opara, daya daga cikin manyan ‘yan jarida a Najeriya.

Ya ce suna fatan ci gaba da yada irin tunanin da Opara ya tsaya tsayin daka akai a rayuwarsa.

Ya kuma ce suna fatan wannan taro zai taimaka wajen samar da mafita ga matsalolin da za su iya tsara makomar Najeriya da ci gabanta.

Hadimin Buhari ya soki masu kushe Muslim/Muslim

Kun ji cewa tsohon hadimin Muhammadu Buhari ya bukaci wadanda suka soki mulkin Muslim-Muslim na Bola Tinubu su nemi gafara.

Kara karanta wannan

Dattawan Arewa sun raba gari da gwamnatin Tinubu kan kama Farfesa Yusuf

Bashir Ahmad ya fadi haka ne bayan shugaban CAN na Arewa ya ce Kiristoci na jin dadin mulkin Tinubu a yanzu.

Yakubu Pam ya ce zaluncin da Kiristoci suka fuskanta a gwamnatocin baya ya ragu, yana yabawa Tinubu kan kokarinsa na hada kowa da kowa a mulki.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

iiq_pixel