Wani Bawan Allah da Ya Musulunta Ya Fara Funkantar Matsala da Matarsa a Abuja

Wani Bawan Allah da Ya Musulunta Ya Fara Funkantar Matsala da Matarsa a Abuja

  • Wani magidanci mai suna Yahaya ya kai ƙarar matarsa gaban kotu a Abuja, ya nemi a raba aurensu saboda banbancin addini
  • Ya shaidawa alƙali ya auri matar ne lokacin yana Kirista, daga bisani kuma ya musulunta, tun daga nan zaman lafiya ya bar gidansa
  • Ya roki kotun ta raba auren sannan ta ba shi damar riƙe ɗaya daga cikin ƴaƴa biyu da suka haifa a zaman aurensu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Wani magidanci mai suna Yahaya ya nemi kotu ta raba aurensa da matarsa, Adenike, bisa dalilin banbancin addini.

Yahaya ya bayyana cewa yana bin addinin Kiristanci lokacin da suka yi aure, amma daga baya ya Musulunta.

Kotu.
Magidanci ya nemi a raba aurensa da matar da ya aura kafin ya musulunta Hoto: Court
Asali: Twitter

Rahoton Tribune Nigeria ya nuna cewa matarsa ta ki aminta su koma addinin Musulinci tare, lamarin da ya haifar da matsaloli a tsakaninsu.

Kara karanta wannan

Rikakken dan bindiga ya tuba daga barna bayan sakin wadanda ya kama, ya sauya suna

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Magidanci ya fara fuskantar matsala a gida

A cewarsa, wannan banbanci ya sa zamansu ya fara wargajewa, har suka daina samun fahimta da mu'amala a tsakaninsu, suka koma rayuwa kamar baƙi a gida ɗaya.

Baya ga bukatar rabuwa, Yahaya ya roki kotu da ta ba shi damar rike ɗaya daga cikin ‘ya’yansu biyu, yayin da matarsa za ta riƙe ɗayan.

Abin da Yahaya ya faɗawa Kotu

A gaban kotu, Yahaya ya ce:

“Mai shari’a, ba mu yi biki ba lokacin aurenmu, kuma ban biya sadaki ba. A lokacin da muka yi aure, ni Kirista ne, amma daga baya na karɓi addinin Musulunci.
“Matata ta ki yarda da wannan canji, kuma ta hana mu zauna lafiya. Ta daina kula da ni, ta daina yin ayyukan gida, kazanta ta yi yawa a gidan.
“A yanzu, babu fahimtar juna a tsakaninmu kuma ba mu ma cika magana da juna ba. Muna rayuwa ne kamar baƙi a gida guda.

Kara karanta wannan

'Na rasa budurcina': Bobrisky ya fadi yadda ya dirka wa budurwa ciki a jami'a

Buƙatun da magidancin ya nema a kotu

Magidancin ya roki alkalin kotun ya kashe auren, sannan ya raba masu ƴaƴa biyu da suka haifa a zaman aurensu.

“Ina rokon wannan kotu mai daraja da ta raba aurenmu kuma ta bani damar riƙe ɗaya daga cikin ‘ya’yanmu biyu, matata ta riƙe ɗayan.
"Zan kuma rika ba da N10,000 duk wata domin ciyar da yaron da ke tare da ita," in ji shi.

Bayan sauraron karar, alkalin kotun, Mai shari'a S.M. Akintayo, ta daga shari’ar zuwa wani lokaci na gaba.

Magidanci ya yi barazanar faɗawa rijiya

A wani rahoton, kun ji cewa wani magidanci, Mista Isiaka Azeez ya nemi kotu ta raba aurensa da mai ɗakinsa bayan shekaru 40 suna tare.

Azeez ya yi barazanar cewa zai fada rijiya idan kotun ba ta amince da bukatarsa ta neman raba auren ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

iiq_pixel