Sauƙi Ya Fara Bayyana, An Fara Sayen Shinkafa, Wake da Masara a Farashi Mai Araha

Sauƙi Ya Fara Bayyana, An Fara Sayen Shinkafa, Wake da Masara a Farashi Mai Araha

  • Farashin abinci kamar shinkafa, wake, doya, garri, da taliya sun fara raguwa a kasuwannin Kaduna idan aka kwatanta da tsadar 2024
  • Buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 wanda a baya ake siyar da shi N125,000 zuwa N130,000, yanzu ya ruguzo zuwa N120,000-N123,000
  • ‘Yan kasuwa sun fara fitar da kayayyakinsu saboda tsoron asara, ganin cewa farashin kayan abinci ya fara sauka a farkon shekara

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kaduna - Mai yiwuwa an shiga 2025 da kafar dama yayin da rahotanni suka nuna an fara samun sauƙin tsadar kayan abinci a jihar Kaduna.

Bayanai sun nuna cewa kwanaki 17 da shigowar sabuwar shekara, kayan abinci sun fara araha fiye da yadda aka baro 2024 a jihar.

Kayan abinci.
Farashin kayan abinci ya fara arha a manyan kasuwannin Kaduna Hoto: Contributor
Source: Getty Images

Binciken da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya gudanar ya nuna cewa farashin kayan abinci kamar hatsi da sauran kayan masarufi sun fara raguwa a kasuwannin Kaduna.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga 30 sun shiga har cikin daki sun sace mata da miji a Abuja

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Farashin kayan abinci ya fara araha

Rahoton ya tabbatar da cewa farashin kayan abinci kamar shinkafa, wake, doya, garri da taliyar yara sun sauka duk da ba wani rangwame sosai aka samu ba.

A kasuwar Sheikh Abubakar Gumi, wacce ita ce babbar kasuwar Kaduna, buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 da aka sayar N125,000 zuwa N130,000 a baya, yanzu ana sayar da shi tsakanin N120,000 zuwa N123,000.

Haka kuma, doya wacce farashin sa yake N7,00 a shekarar 2024, yanzu ta sauka zuwa tsakanin N5,000 zuwa N6,000, yayin da kananan doya suka sauka zuwa N2,500.

Yadda wake da shinkafa suka sauka

Kwanon wake mai cin kofi huɗi wanda a baya ake siyarwa tsakanin N3,000 zuwa N3,500, yanzu ya ƙara arha duk kwano ɗaya ya dawo N2,500, The Nation ta kawo.

Haka zalika, kwanon garri ya sauko zuwa N1,200 daga farashin da aka rika saye a kwanakim baya tsakanin N1,400 zuwa N1,500.

Kara karanta wannan

'Yan kasuwa sun sanar da saukar farashin fetur bayan karyewar abinci

Wasu daga cikin kwastomomi masu sayen kayan abinci a kasuwar Kaduna sun shaidawa NAN cewa suna fatan wannan sauƙi da aka fara samu ya ɗore.

Hafsat Muhammad ta ce yanzu tana sayen lokar shinkafa a N2,100, sabanin farashinsa na baya N2,400, lokar masara da ake sayarwa N1,200 a baya, yanzu ta dawo N900.

Ƴan kasuwa sun fara fito da kayansu

Hajiya Ummi Shuaibu, wata ‘yar kasuwa, ta ce ta sayi buhunan masara bayan girbi da niyyar sake siyarwa bayan wasu watanni, amma ta canza ra'ayi tun da farashin kayan abinci ya fara sauka.

“Na yi tsammanin farashin zai tashi kamar na bara, amma hakan bai faru ba, don haka dole ne in fitar da kayan hannuna domin kar na yi asara.
“Buhun masara wanda a baya yake kan N60,000 yanzu yana tsakanin N50,000 zuwa N55,000, shi ya sa nake son sayarwa da wuri,” in ji ta.

Farashin shinkafa da wake ya sauka a Akure

Kun ji cewa farashin kayayyaki ya fara sauka a Akure, babban birnin jihar Ondo da ke Kudu maso Yammacin Najeriya.

Kara karanta wannan

Abubuwan da 'yan Najeriya suka fada bayan Buhari ya yi kyautar daloli

An ruwaito cewa farashin taliya, shinkafa da wake duk sun yi ƙasa amma kuma farashin manja da tattasai sun yi tashin gwauron zabi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262