An Shiga Rudani da Jirgin Sama Ya Yi Mummunan Hatsari a Najeriya, an Rasa Rayuwa

An Shiga Rudani da Jirgin Sama Ya Yi Mummunan Hatsari a Najeriya, an Rasa Rayuwa

  • Jirgi mai saukar ungulu ta fadi a birnin Port Harcourt da ke jihar Rivers inda mutane uku suka rasa rayukansu dalilin haka
  • Lamarin ya faru ne a yau Alhamis 24 ga watan Oktoban 2024 inda jirgin ke dauke da mutane guda takwas
  • Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin sufurin jiragen sama, Odutayo Oluseyi shi ya tabbatar da haka a yau

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Rivers - Aƙalla mutane uku ne suka rasa rayukansu bayan faduwar jirgin sama mai saukar ungulu.

Jirgin ya fadi ne a birnin Port Harcourt da ke jihar Rivers a yau Alhamis 24 ga watan Oktoban 2024.

Jirgin sama mai saukar ungulu ya yi hatsari
Mutane 3 sun mutu yayin da jirgin sama ya yi hatsari. Hoto: @fkeyamo.
Asali: Getty Images

An rasa rayuka bayan faduwar jirgin sama

Kara karanta wannan

An shiga jimami bayan sojojin Najeriya sun rasu a wani hatsari

Kakakin ma'aikatar sufurin jiragen sama, Odutayo Oluseyi shi ya tabbatar da haka a yau Alhamis 24 ga watan Oktoban 2024, cewar TheCable.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar ta ce jirgin na dauke ne da mutane takwas ne yayin da tsautsayin ya faru a Port Harcourt, Punch ta ruwaito.

Oluseyi ya ce jirgin ya taso ne daga sansanin sojoji na Port Harcourt zuwa rijiyar mai inda ya fada kogi.

An tsamo gawarwakin mutum 3 a Rivers

Ma'aikatar ta ce an tsamo gawarwakin mutum guda uku inda ake cigaba da aikin ceto domin nemo sauran mutanen.

"Jirgin sama mai saukar ungulu dauke da lamba, 5NBQG ya taso ne daga sansanin sojoji a Port Harcourt zuwa wata rijiyar mai."
"Jirgin mai dauke da mutane takwas ya gamu da tsautsayin ne a yankin Inda ya fada kogin Atlantic Ocean."

- Cewar sanarwar

Kara karanta wannan

Bayan hadarin Kano Pillars, mutane kusan 20 da ke hanyar zuwa Abuja sun gamu da ajali

An tabbatar cewa Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo yana bakin korari domin dakile asarar rayuwa da samun raunuka.

Fasinjoji sun tsallake rijiya ta baya

Kun ji cewa an samu afkuwar masifar hadarin jirgin sama a jihar Adamawa bayan fashewar tayoyin wani jirgin saman.

Fasinjoji 199 a jirgin Max Air ne su ka tsira yayin da tayoyin jirgin guda shida su ka yi bindiga ana kokarin tashi.

Yanzu dai an tabbatar babu ko mutum daga da ya samu rauni, kuma tuni hukumomi su ka fara binciken fashewar tayoyin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.