Hukumar FIRS Za Ta Dauki Ma’aikata, Ta Bayyana Wadanda Suka Cancanci Neman Aikin

Hukumar FIRS Za Ta Dauki Ma’aikata, Ta Bayyana Wadanda Suka Cancanci Neman Aikin

  • Hukumar tara kudin shiga ta tarayya (FIRS) ta aika sako ga 'yan Najeriya da ke son yin aikin gwamnati a matsayin jami'an haraji
  • FIRS ta bayyana cewa za ta dauki ma'aikata a bangaren jami'an haraji na daya da na biyu kuma tana neman masu sha'awar aikin
  • Hukumar ta nemi wadanda ke son bajintarsu a aikin gwamnati da bayar da gudummawa ga ci gaban kasa da su nemi aikin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - A yayin da matasan Najeriya ke korafin rashin ayyukan yi, hukumar tara kudin shiga ta tarayya (FIRS) ta sanar da fara daukar ma'aikata.

Hukumar FIRS ta bayyana cewa tane neman matasan da suka kammala karatun gaba da sakandare domin su nemi aikin jami'an haraji a hukumarta.

Kara karanta wannan

Bayan kara kudin fetur, Tinubu ya shirya kakabawa 'yan Najeriya wani sabon haraji

Hukumar FIRS ta yi magana kan daukar aiki a bangaren jami'an haraji
Hukumar FIRS za ta dauki aiki a bangaren jami'an haraji, ta yi karin bayani. Hoto: @FIRSNigeria
Asali: Facebook

Hukumar FIRS za ta dauki ma'aikata

Hukumar ta sanar da hakan ne a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X (tsohon Twitter) a ranar Litinin, 21 ga Oktoba, 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar ta ce hukumar za ta dauki ma'aikata a matakin jami'in haraji na daya da na biyu.

A cikin sanarwar, FIRS ta bayyana cewa nan gaba kadan za ta fitar da cikakkun bayanai game da tsarin neman guraben aikin.

Za a ji lokacin fara nema da gamawa da sauran bayanai a shafinta na intanet.

“Hukumar tara kudin shiga ta tarayya (FIRS) hukuma ce da ke ba kowanne dan Najeriya da ya cancanta damar yin aiki da ita."

- Inji sanarwar.

"Wadanda suka cancanta su nema" - FIRS

Sanarwar ta bayyana cewa:

"Muna bukatar matasan da suke da daraja da kuma burin samun ci gaba a aiki, sannan muna neman wadanda suke da basira a kididdiga, warware matsaloli da kwarewa a sadarwa.

Kara karanta wannan

CNG: Gwamnati ta bayyana abin da ya jawo wata mota mai amfani da gas ta fashe

"Muna ƙarfafa guiwar duk wadanda suka san sun cancanta da su nemi aikin ba tare da la'akari da jinsi, kabila, ko asalinsu ba.
"Ku kasance tare damu domin samun ƙarin bayanai, kuma muna godiya da kuka nuna sha'awarku ta yin aiki tare da hukumar FIRS."

Gwamna zai dauki ma'aikata 17,000

A wani labarin, mun ruwaito cewa gwamnan Kano, Abba Kabiru Yusuf ya sanar da shirinsa na daukar sababbin ma'aikata har 17,000 a fadin jihar.

Gwamnatin Kano za ta ɗauki jami'ai mafarauta aikin tsaro a wani ɓangare na kokarin bunƙasa harkokin ilimi da ke fuskantar barazanar tsaro.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.