'Yadda Mahaifinmu Ya Hana Mu Saka Rai game da Gadonsa': Tsohon Gwamna Ya Magantu

'Yadda Mahaifinmu Ya Hana Mu Saka Rai game da Gadonsa': Tsohon Gwamna Ya Magantu

  • Tsohon gwamnan Osun ya bayyana yadda mahaifinsu ya gargade su kan arzikin da ya bari saboda ka da kowa ya saka rai
  • Olagunsoye Oyinlola ya ce sun kasance su 64 a cikin iyalansu amma babu mai maganar rabon gado har zuwa yanzu
  • Oyinlola ya ce mahaifinsu wanda basarake ne kafin rasuwarsa ya ce babu wani gata da ya bar musu illa ilimi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Osun - Tsohon gwamnan jihar Osun, Olagunsoye Oyinlola ya yi magana kan gadon gidansu.

Oyinlola ya ce mahaifinsu wanda basarake ne ya yi musu gargadi kan dogaro da arzikinsa a matsayin gado.

Tsohon gwamna ya fadi wasiyya da mahaifinsu ya yi musu
Tsohon gwamnan Osun, Olagunsoye Oyinlola ya yi magana kan wasiyyar mahaifinsu. Hoto: Olagunsoye Oyinlola.
Asali: Facebook

Tsohon gwamna ya magantu kan wasiyyar mahaifinsu

Kara karanta wannan

Amaechi ya fadi rikicinsa da tsohon gwamnan APC har ya kai shi kara wurin Buhari

Tsohon gwamnan ya bayyana haka ne a taron wayar da kan dalibai a Kwalejin kiwon lafiya a Okuku da ke jihar, cewar The Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Oyinlola ya ce mahaifinsu da ya rike sarautar Olokuku a garin Okuku ya shawarci 'ya'yansa 64 kan saka rai a arzikinsa.

Dan Sarkin ya ce marigayin ya fada musu cewa duk mai jiran ya ci gadonsa yana bata lokacinsa ne kawai.

Har ila yau, Oyinlola ya ce mahaifin nasu ya ce ya bar musu ilimi wanda shi ne gaban komai a rayuwa.

'Mahaifinmu ya gargade mu kan gadonsa ' - Oyinlola

"Lokacin da nake yaro kafin mahaifina wanda basarake ne ya rasu, ya ce duk mai jiran cin gadonsa yana bata lokacinsa ne."
"Ya ce babu abin da ya bar mana a matsayin yayansa 64 a rayuwa game da arziki ko gado da ya wuce ilimi."

Kara karanta wannan

Yadda tsohon sanata ya rasu jim kadan bayan kammala addu'o'i a gadon asibiti

"Har yanzu ilimi ne ke riƙe da gidanmu, yau shekaru 64 da mutuwarsa, babu wanda ya ke tunanin raba gado."

- Olagunsoye Oyinlola

Gwamna ya ce rawa na burge shi

Kun ji cewa Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun ya ce yana ƙaunar rawa ne saboda tana faranta masa rai amma sauke nauyin talakawa ya fi masa daɗi.

Adeleke ya bayyana haka ne yayin da yake martani ga wani mutumi, wanda ya yaba da ƙoƙarin gwamnan da sukar da yake sha daga ƴan adawa.

Gwamnan ya ƙara da cewa gwamnatinsa na ci gaba da gyaran asibitoci da gina hanyoyi a kowace ƙaramar hukuma a Osun.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.