‘Ya Kashe Mata Ya Wulaƙanta Gawarsu,’ An Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga

‘Ya Kashe Mata Ya Wulaƙanta Gawarsu,’ An Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga

  • An kama wani ƙasurgumin ɗan bindiga mai suna Ogunnaike Philip a jihar Ogun bayan ya hallaka wasu yan mata guda uku
  • Ana zargin cewa Ogunnaike Philip ya kashe yan matan ne da wulaƙanta gawarsu har sai da suka fara ruɓewa bayan a wurgar da su
  • Rahotanni sun nuna cewa Ogunnaike Philip ya shahara da kashe rayukan da ba su ji ba, ba su gani ba a yankuna da dama na jihar Ogun

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Ogun - Yan Amotekun a Kudu maso Yamma sun kama wani dan bindiga da ake zargi da kisan wasu mata.

Ana zargin cewa Ogunnaike Philip ya yi wa wasu yan mata ne kisan gilla kuma ya wulakanta gawarsu.

Kara karanta wannan

CNG: Ana jimamin hatsarin Jigawa, mota mai amfani da gas ta fashe a gidan mai

Jihar Ogun
An kama dan bindiga a Ogun. Hoto: Legit
Asali: Original

Jaridar Daily Trust ta wallafa cewa jami'in yada labaran Amotekun, Adeleye Abiodun Adewale ne ya fitar da sanarwar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dan bindiga ya kashe yan mata

Yan Amotekun a jihar Ogun sun kama wani matashi mai shekaru 29 bisa zargin kisan gilla wa wasu yan mata uku.

Ana zargi Ogunnaike Philip ya kashe yan matan ne a jihar Ogun a lokuta mabanbanta ciki har da wata budurwa mai shekaru 18.

Yadda aka samo matan da aka kashe

Yan Amotekun sun bayyana cewa an samo gawar wata budurwa mai suna Taiwo ne a wani jeji a kusa da unguwar Egbewa a cikin wani kango.

Haka zalika an samo gawar daya budurwar mai suna Fatoki Seun a wani jeji kusa da unguwar Oki-Oja a jihar.

Rahotanni sun nuna cewa yan Amotekun sun samo gawar yan matan ne bayan sun fara ruɓewa a wajen da ya wurgar da su.

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun yi ƙawanya a kauye cikin dare, sun kashe mutane

An mika gawar yan mata asibiti

Daily Post ta wallafa cewa yan Amotekun sun ce a yanzu haka an mika gawar yan matan a babban asibitin yankin.

Kakakin Amotekun Adeleye Abiodun Adewale ya bayyana cewa dan bindigar ya shafe wata daya a yankin kafin a gano barnar da ya yi.

Za a fadada yaki da yan bindiga

A wani rahoton, kun ji cewa ministan tsaron Najeriya, Muhammad Badaru Abubakar ya bayyana shirin yakar yan bindiga da suka yi.

Muhammad Badaru Abubakar ya bayyana shirin ne yayin ganawa da gwamnan jihar Kaduna domin neman hadin kan shugabannin Arewa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng