Kotu Ta Yi Hukunci kan Zargin Hon. Doguwa da Kisan Kai, an Ci Tarar Abba Kabir

Kotu Ta Yi Hukunci kan Zargin Hon. Doguwa da Kisan Kai, an Ci Tarar Abba Kabir

  • Yayin da ake zargin Hon. Alhassan Ado Doguwa da kisan kai tun zaben 2023, Kotun Daukaka Kara ta wanke shi
  • Kotun karkashin jagorancin Mai Shari'a, Donatus Okorowo ya yi fatali da korafin gwamnatin jihar Kano kan doguwa
  • Alkalin ya kuma umarci gwamnatin jihar ta guji kamawa da tsarewa ko hukunta Doguwa inda ya ci tararta

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Kotun Daukaka Kara ta yi hukunci kan zargin Hon. Alhassan Ado Doguwa da kisan kai a zaben 2023.

Kotun ta tabbatar da wanke dan Majalisar daga jihar Kano inda ta haramtawa Abba Kabir kama shi da kuma cin zarafinsa.

Kotu ta wanke dan Majalisar Tarayya kan zargin kisan kai
Kotun Daukaka Kara ta wanke Hon. Alhassan Ado Doguwa kan zargin kisan kai a zaben 2023. Hoto: Hon. Ado Doguwa, Abba Kabir Yusuf.
Asali: Facebook

Zargin kisan kai: Kotu ta wanke Hon. Doguwa

Kara karanta wannan

Gwamnan APC ya shiga matsala da ɗan Majalisa ya maka shi a kotu da hadimansa 2

Alkalin kotun, Mai Shari'a, Donatus Okorowo shi ya yanke hukuncin inda ya umarci biyan Doguwa diyyar kudi har N25m, cewar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kotun ta yi fatali da korafin gwamnatin jihar Kano kan shigar da Hon. Doguwa kara da zargin kisan kai a zaben 2023.

Hon. Doguwa ya ce korafin da aka shigar game da shi kan rigimar zaben 2023 an yi bincike kuma yan sanda da babbar kotun jihar Kano sun wanke shi.

Hon. Doguwa ya yi godiya ga Ubangiji

Da ya ke martani kan hukuncin kotun, Hon. Doguwa ya yi godiya ga Ubangiji tare da nuna kwarin guiwa a bangaren shari'a a Najeriya, Thisday ta ruwaito.

"Mun godewa Allah da ya sake tabbatar da gaskiyarmu da kuma kare mu daga sharrin makiya yan adawa."
"Ina kira ga magoya bayana da su yi murnar wurin godewa Allah game da nasarar da muka samu da kaucewa take doka da oda."

Kara karanta wannan

Amaechi: Kalaman Ministan Buhari sun yi wa APC zafi, an zarge shi da tada hargitsi

- Hon. Alhassan Ado Doguwa

2027: Doguwa ya caccaki Sanata Rabiu Kwankwaso

Kun ji cewa dan Majalisar Tarayya da ke wakiltar Tudun Wada/Doguwa a Kano ya mayarwa Rabiu Musa Kwankwaso martani.

Hon. Alhassan Doguwa ya ce har yanzu Kwankwaso a kidime yake bayan faduwa zaben 2023 a hannun Bola Tinubu.

Doguwa ya shawarci Kwankwaso ya mayar da hankali kan zaben 2027 inda za a yi masa ritaya gaba daya a siyasa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.