'Yadda Bello Turji Ke Nadawa da Sauke Dagatai a Sokoto Lokacin da Ya So'

'Yadda Bello Turji Ke Nadawa da Sauke Dagatai a Sokoto Lokacin da Ya So'

  • Rahotanni sun tabbatar da cewa dan ta'adda, Bello Turji shi ke iko da mafi yawan ƙauyuka a jihar Sokoto da ke Arewacin Najeriya
  • Shugaban karamar hukumar Isa, Alhaji Sharifu Kamarawa shi ya tabbatar da haka ga ƙaramin Ministan tsaro, Bello Matawalle
  • Kamarawa ya ce dan ta'addan shi ke saukewa da kuma nada wasu daga cikin dagatai a mafi yawan ƙauyuka a jihar ta Sokoto

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Sokoto - Shugaban karamar hukuma a jihar Sokoto ya tabbatar da cewa har yanzu wasu yankuna na karkashin ikon yan ta'adda.

Shugaban karamar hukumar Isa a jihar, Alhaji Sharifu Kamarawa shi ya tabbatar da haka ga karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle.

An fadi yadda Bello Turji ke nadi da kuma sauke Dagatai
Shugaban karamar hukuma a Sokoto ya tona asirin yadda Bello Turji ke sheke ayarsa. Hoto: @Ahmedaliyuskt.
Asali: Twitter

Sokoto: An gano yadda Turji ke ikonsa

Daily Trust ta ruwaito Kamarawa na cewa dan ta'adda, Bello Turji yana saukewa da kuma daura dagatai a kauyuka.

Kara karanta wannan

An kaure a Majalisar Tarayya kan rigimar sarauta da aka bukaci Tinubu ya tsoma baki

Hon. Kamarawa ya ce Gabashin Isa an fi samun matsala inda yan ta'adda ke da iko sosai a yankin.

Hakan ya biyo bayan ziyarar karamin Ministan tsaro jihar Sokoto a kokarin dakile yan ta'addan da suka addabi al'umma.

Yadda Turji ke nadi da sauke dagatai

"A nan garin Isa muna zaune lafiya amma a Gabashin Isa har yanzu yan bindiga ke da iko inda suke saukewa da nadin dagatai."
"Mu na rokon jami'an sojoji a sansanin Kagara su kawo dauki a wadannan wurare, a baya muna shi kafin aka dauke shi."

- Hon. Kamarawa

Hon. Kamarawa ya ce tun bayan kisan rikakken dan ta'adda, Halilu Sububu, an dan samu sauki kan hare-haren yan bindiga a yankunan inda ya ce mutane suna yin harkokinsu.

Gwamnatin Sokoto ta magantu kan Bello Turji

Mun ba ku labarin cewa bayan ganin sabon bidiyon dan ta'adda, Bello Turji, gwamnatin Sokoto ta yi magana kan dalilin aika-aikar.

Kara karanta wannan

Ministan tsaro ya fadi abin da zai faru ga masu ba yan ta'adda bayanai

Gwamnatin Sokoto ta ce Turji ya rikide ne saboda ganin shirin karar da su da Gwamna Ahmed Aliyu ke yi.

Hakan ya biyo bayan fitar da wani sabon bidiyo da kasurgumin dmà ta'adda, Bello Turji ya yi a ranar Laraba 4 ga watan Satumbar 2024.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.