Murna yayin da Gwamna Ya Sanar da Lokacin Fara Biyan Mafi Karancin Albashi

Murna yayin da Gwamna Ya Sanar da Lokacin Fara Biyan Mafi Karancin Albashi

  • Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo ya ba ma'aikata tabbacin cewa zai fara biyan mafi ƙarancin albashi na N70,000
  • Gwamna Makinde ya bayyana cewa zai ci gaba da mayar da hankali wajen jindaɗin ma'aikatan jihar ta yadda za su ji daɗin gudanar da ayyukansu
  • Ya bayyana hakan ne a wajen bikin ranar malamai ta duniya na shekarar 2024 wanda aka gudanar a ranar Asabar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Oyo - Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya bayar da tabbacin cewa gwamnatinsa za ta fara biyan mafi ƙarancin albashi na N70,000.

Gwamna Seyi Makinde ya bayyana cewa zai fara biyan mafi ƙarancin albashin da zarar an daidaita batun ƙarin da za a yi a albashin.

Kara karanta wannan

Kaico: Ana tsaka da cin amarci, ango ya kashe amaryarsa ta hanya mai ban tausayi

Makinde zai biya mafi karancin albashi
Gwamnan Oyo zai biya ma'aikata mafi karancin albashi Hoto: Seyi Makinde
Asali: Facebook

Gwamna Makinde ya kuma sanar da ƙarawa ma’aikata albashin N25,000 da kuma ƙarin albashin N15,000 ga ƴan fansho na watanni uku, cewar rahoton jaridar Tribune.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Makinde zai biya ma'aikata N70,000

Gwamna Makinde ya bayyana hakan ne a ranar Asabar a yayin bikin ranar malamai ta duniya na shekarar 2024 wanda aka gudanar a daƙin taro na NUT a Apata cikin birnin Ibadan, babban birnin jihar, rahoton Vanguard ya tabbatar.

"A kan mafi ƙarancin albashi, za a fara tattaunawa a mako mai zuwa kuma za mu biya mafi ƙarancin albashin N70,000. Amma za mu tattauna kan ƙarin da za a yi. Tawagar mu da ta ƙungiyar NLC za su zauna domin tattaunawa a kai."

- Seyi Makinde

Gwamna Makinde ya yabawa malamai

Gwamna Makinde ya yabawa malaman jihar kan irin ɗimbin goyon bayan da suka ba shi a lokacin zaɓen da ya gabata da kuma gudunmawar da suke badawa wajen gina jihar.

Kara karanta wannan

Bam ya fashe a sakatariyar jam'iyyar APC, an samu bayanai

Gwamna Makinde ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da ba da fifiko kan jin daɗin malamai da ma’aikatan gwamnati a jihar ta yadda za su ci gaba da gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Gwamna Soludo zai fara biyan N70,000

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Anambra, Farfesa Charles Chukwuma Soludo ya shirya biyan ma'aikata mafi karancin albashi na N70,000.

Gwamna Charles Soludo ya yi alƙawarin fara biyan sabon albashin a ƙarshen watan Oktoban shekarar 2024.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng