NiMet: Za a Zabga Ruwan Sama daga Laraba zuwa Juma'a a wasu Jihohin Arewa 16
- Ana sa ran za a sha mamakon ruwan sama tare da tsawa daga ranar Laraba zuwa Juma'ar makon nan a wasu jihohi 16 na Arewa
- Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMet) ta yi hasashen cewa ruwan zai sa a lokuta daban daban a wadannan jihohi
- Jihohin da ake sa ran za su samu ruwan saman sun hada da Adamawa, Taraba, Sokoto, Kebbi, Zamfara, Kaduna da dai sauransu
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Abuja - Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMet) ta yi hasashen cewa za a zabga ruwan sama hade da tsawa daga ranar Alhamis zuwa Asabar a wasu jihohin kasar nan.

Kara karanta wannan
Murnar samun 'yanci: Gambo Sawaba da fitattun mata 2 da su ka jijiga siyasar Najeriya
A yayin da ruwan saman zai sauka da safiyar ranakun uku, NiMet ta ce wasu jihohin za su samu nasu ruwan ne da yammacin kowace rana.

Asali: Getty Images
An fitar da hasashen yanayi na NiMet a ranar Talata, 1 ga watan Oktobar 2024 a Abuja kamar yadda jaridar Premium Times ta ruwaito.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ruwan sama a ranar Laraba
NiMet ta yi hasashen ruwan sama da tsawa a sassan jihohin Adamawa, Taraba, Sokoto, Kebbi, Zamfara da Kaduna a safiyar Laraba.
A cewar NiMet, ana sa ran za a yi ruwa da tsawa da yammacin Laraba a wasu sassan jihohin Bauchi, Adamawa, Kaduna, Katsina, Taraba, Yobe, Zamfara, Borno da Kebbi.
“A shiyyar Arewa ta tsakiya, ana hasashen ruwa da tsawa a sassan babban birnin tarayya, jihohin Neja, Nasarawa da Binuwai da safe.
“Da yammaci kuwa, ana sa ran za a yi ruwa da tsawa a babban birnin tarayya, jihohin Neja, Kogi, Kwara, Benuwai, Filato da Nasarawa."
- A cewar hasashen.
Ruwan sama a ranar Alhamis
Hukumar NiMet ta yi hasashen ruwa da tsawa a sassan jihohin Adamawa, Taraba da Kebbi da safiyar ranar Alhamis.
An yi hasashen za a yi ruwa da tsawa a wasu sassan jihohin Kaduna, Adamawa, Katsina, Kebbi, Taraba, Sokoto da Zamfara a yammacin ranar.
“A yankin Arewa ta tsakiya, ana iya samun ruwa da tsawa a sassan babban birnin tarayya, jihohin Neja, Kogi, Kwara, Benuwai da Nasarawa da safe.
“Yayin da kuma daga takewar rana har zuwa yammaci ake sa ran za a yi ruwa da tsawa a sassan babban birnin tarayya, jihohin Neja, Kogi, Benuwai da Nasarawa.
- A cewar NiMet.
Ruwan sama a ranar Juma'a
A cewar NiMet, ana sa ran za a yi ruwa da tsawa a sassan jihohin Zamfara, Sokoto da Kebbi da safiyar ranar Juma'a.
NiMet ta ce:
“A yankin Arewa ta tsakiya ana sa ran saukar ruwa da tsawa a sassan Nasarawa, Kogi, Kwara, Neja da kuma babban birnin tarayya da safe.

Kara karanta wannan
Kaduna: An zargi sojoji da sake jefa bama bamai a masallaci aka kashe bayin Allah
“A yammacin ranar, ana sa ran za a yi ruwa da tsawa a sassan Nasarawa, Kogi, Benuwai, Kwara, Neja da kuma babban birnin tarayya."
Ruwan sama a Kano da jihohi 16
A wani rahoton makamamancin wannan, mun ruwaito cewa hukumar NiMET ta sanar da cewa za a tafka mamakon ruwa a jihohi 17 na Arewa.
Hukumar ta gargadi mazauna wadannan jihohi da su yi taka tsantsan musamman wadanda ke a yankunan gabar tekuna domin gujewa ambaliyar ruwa.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng